“Ana Fama Har Yau”: Shehu Sani Ya Magantu Kan Maida N794,000 Mafi Karancin Albashi

“Ana Fama Har Yau”: Shehu Sani Ya Magantu Kan Maida N794,000 Mafi Karancin Albashi

  • Tsohon 'dan majalisar tarayyar Najeriya, Shehu Sani, ya ce har yanzu jihohi da dama na fama da yadda za su biya ma'aikata mafi karancin albashi na N30,000
  • Sani ya ce yadda za a biya mafi karancin albashi na sama da N700,000 da 'yan kwadago suka bukata wani abu ne da ya kamata a tattauna a kai
  • Jaridar Legit ta rahoto cewa kungiyoyin kwadago na NLC da TUC na so a kara albashin wata da kyau domin magance halin da ake ciki na matsin rayuwa a Najeriya

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amura

FCT, Abuja - Shehu Sani, 'dan majalisa da ya wakilci Kaduna ta tsakiya a baya, ya nuna shakku kan yiwuwar biyan mafi karancin albashi na N794,000 a Najeriya.

Kara karanta wannan

Ma'aikatan Akwa Ibom sun ce lallai N850, 000 za su karba a mafi karancin albashi

A wallafar da ya yi a shafinsa na Twitter a ranar Juma'a, 8 ga watan Maris, Sani ya bayyana cewa da kyar jihohi da dama ke iya biyan mafi karancin albashi na N30,000.

Shehu Sani ya magantu kan karancin albashi
Shehu Sani ya nuna shakku kan mafi karancin albashin da 'yan kwadago suka nema Hoto: Senator Shehu Sani
Asali: Facebook

Jigon na PDP, ya ce ya kamata a yi muhawara kan yadda za a biya mafi karancin albashi na N700,000 da 'yan kwadago suka bukata.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shehu Sani ya rubuta:

"Da mafi karancin albashin 30k, har yanzu jihohi da dama na fama da yadda za su biya albashi. Yadda za a biya mafi karancin albashi na 700k da 'yan kwadago suka bukata abu ne da ya kamata a yi muhawara a kai.
"Buga karin takardun kudi abu ne ma da bai kamata gwamnati ta kawo tunaninsa ko a rai ba.

Kungiyar kwadago ta gabatar da bukatarta

A halin da ake ciki, Legit Hausa ta rahoto cewa kungiyar kwadago ta NLC ta bukaci mafi karancin albashi N794, 000 ga ma'aikatan yankin Kudu maso Yamma.

Kara karanta wannan

Kungiyar NLC ta bukaci N794,000 ga ma'aikata a yankin Tinubu, bayanai sun fito

Shugabar kungiyar a yankin, Funmi Sessi ita ta bayyana haka a yau Alhamis 7 ga watan Maris a Legas.

Ma'aikatan Akwa Ibom sun nemi N850,000

A wani labarin kuma, kungiyoyin kwadago na NLC da TUC sun bukaci a biya ma’aikatan jihar Akwa Ibom N850,000 a matsayin mafi karancin albashi.

Shugaban kungiyar NLC na jihar, Kwamared Sunny James ne ya bayyana haka yayin taron jin ra’ayin jama’a da gwamnatin tarayya ta shirya kan mafi karancin albashi a garin Uyo, a ranar Alhamis, 7 ga watan Maris.

Asali: Legit.ng

Online view pixel