Manyan Kiristocin Kaduna Sun Waiwayi Sojoji, Sun Rataya Aikin Kare Al’ummarsu a Wuyansu

Manyan Kiristocin Kaduna Sun Waiwayi Sojoji, Sun Rataya Aikin Kare Al’ummarsu a Wuyansu

  • Manyan addinin Kirista a Kaduna sun bayyana bukatar sojoji su kare al’ummarsu a yanayin da ake ciki yanzu
  • Sun shawarci mazauna Kudancin Kaduna da su rungumi zaman lafiya don ganin ci gaba a yankinsu
  • Jihar Kaduna na daga cikin jihohin Arewacin Najeriya da ke fama da rashin tsaro, musamman a wadannan shekarun

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Salisu Ibrahim kwararren editan fasaha, kudi da al'amuran yau da kullum ne, yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru takwas.

Jihar Kaduna - Shugabannin addinin Kirista a Kudancin Kaduna sun daura alhakin kare rayukan mutanensu akan sojojin Najeriya.

Sun kuma yi kira ga jami’an tsaron da su dage wajen tabbatar da ba a ci gaba da kashe Kiristoci mazauna yankin da ma kasa baki daya ba.

Manyan Kiristoci na neman sojoji su kare kiristoci
Ku kare Kiristocin Kaduna, manyan SCKLA sun magantu | Hoto: @ubasanius, @DefenceInfoNG
Asali: Twitter

Shugabannin a karkashin kungiyarsu ta SCKLA sun kuma bukaci mazauna yankin da su yi watsi da tsohuwar gaba da tashin hankali da ke yankin tare da rungumar zaman lafiya.

Kara karanta wannan

An tsinci gawar wani matashi babu kunne yashe a bola a wata jihar arewa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Waye ya yi wannan kira ga sojoji?

Shugaban kungiyar, Emmanuel Nuhu Kure ne ya yi wannan kiran a wani taron addu’a da aka gudanar a Kafanchan ta jihar Kaduna, The Nation ta ruwaito.

Kure ya yi ishara da cewa, mancewa da duk wata kitimurmurar da ta faru a baya tare da fatan samun ci gaba da gina kasa da kawo ci gaba.

A nasa jawabin, Rabaran Israel Akanji, wanda shine shugaban kungiyar gamayyar Kiristocin Baptist ya karfafa gwiwar al’umma da su kasance masu yiwa kasa addu’a.

Ku zauna lafiya don ku ci gaba a rayuwa

Akanji ya kuma yi kira ga al’umma da su kasance masi aikin isar da sakon ubangiji a ko’ina suka tsince kansu, rahoton jaridar Vanguard.

Wakilin Gwamna Uba Sani na jihar Kaduna, Phoebe Yayi ya jaddada bukatar al’ummar da su zauna lafiya don ganin ci gaba a yankinsu.

Kara karanta wannan

Ana daf da auren malamin makarantar allo, matsafa sun yanke mazakutarsa a Zaria

Jihar Kaduna na daga cikin jihohin da ake yawan samun rikicin kabilanci da bambancin ra’aui a Arewacin Najeriya.

An yanke mazakutar malamin allo a Zaria

A wani labarin, wani rahoto mai daukar hankali ya bayyana yadda wasu matsafa suka yanke mazakutar wani malamin allo a unguwar Awai da ke karamar hukumar Soba ta jihar Kaduna.

An ruwaito cewa, matsafan sun yiwa mutumin mai suna Alaramma Salisu Mai Almajirai yankan rago tare da yi masa aika-aikar yanke mazakutarsa a hanyarsa ta dawowa daga karbo kayan cin angoncinsa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel