Watakila ASUU Ta Tafi Yajin Aiki a 2024 Saboda Tinubu Ya Saba Alkawarin da Ya Dauka

Watakila ASUU Ta Tafi Yajin Aiki a 2024 Saboda Tinubu Ya Saba Alkawarin da Ya Dauka

  • Emmanuel Oshodeke ya ce 7% kacal gwamnatin tarayya ta ware za a kashewa bangaren ilmi a Najeriya a 2024
  • Shugaban kungiyar ta ASUU ya koka kan yadda Bola Tinubu ya saba alkawarin da ya dauka a yayin yakin zabe
  • Farfesa Oshodeke yake cewa an yi alkawarin warewa ilmi 15%, amma ba ayi haka a cikin kasafin kudin badi ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abuja - Ba abin mamaki ba ne a shekara mai zuwa ta 2024, malaman jami’o’in gwamnati su shiga yajin-aikin da aka saba yi a kasar.

Da Punch ta yi hira da shugaban kungiyar ASUU, Farfesa Emmanuel Oshodeke, ya bayyana cewa ana cigaba da yin watsi da sha’anin ilmi.

ASUU.
Hoton wata zanga-zangar 'Yan ASUU a baya Hoto: Getty Images
Asali: Getty Images

ASUU: "Babu abin da ya canza zani"

Farfesa Emmanuel Oshodeke ya ce a lokacin yakin neman zabe, Bola Ahmed Tinubu ya ce zai warewa ilmi 15% a cikin kundin kasafin kudi.

Kara karanta wannan

Neman karbe kujerar Abba Gida-Gida a kotu zalunci ne kawai, Malamin Musulunci

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Bayan ya karbi mulki sai ga shi Mai girma Bola Ahmed Tinubu bai cika alkawarin da ya dauka ba, kungiyar ASUU tace ana nan a gidan jiya.

Farfesan ya ce kungiyar malaman jami’an ta yi tir da jin N2.18tr kacal aka ware domin harkar ilmi a kasafin kudin shekara mai zuwa.

ASUU ta ce ba a cika sharudan UNESCO ba

UNESCO ta bada shawarar ayi wa ilmi tanadin 26%, amma abin da gwamnatin tarayya za ta kashe 7.9% ne rak na kasafin kudin kasar.

Oshodeke ya ba Bola Tinubu shawarar ya zauna da jami’an gwamnatin tarayya domin ganin an kara kason zuwa 15% ko sama da haka.

"Da wannan 7%, babu abin da zai canza zani a bangaren ilmi, kamar yadda yake ne a lokacin Muhammadu Buhari.
Lokacin yakin neman zaben shi, Tinubu ya yi alkawarin kasa kason ilmi, amma bai yi ba."

Kara karanta wannan

Kasafin Tinubu ya fusata Arewa, ba a ware sisi domin aikin wutan Mambilla a 2024 ba

- Farfesa Emmanuel Oshodeke

ASUU za ta tafi yajin-aiki a shekarar 2024?

Daily Post ta rahoto shugaban na ASUU ya ce idan ba ayi komai ba, zuwa shekara mai zuwa zai hada-kan kungiyar domin a dauki mataki.

ASUU tana so a kara albashin malamai, kara shekarun ritaya, bada damar yaye masu PhD, kuma a bambanta su da sauran ma’aikatan gwamnati.

Tinubu zai hana ASUU yajin-aiki

Babu maganar yajin-aikin kungiyar ASUU a jami’o’i idan Bola Ahmed Tinubu ya na kan karagar mulki kamar yadda aka samu labari a baya.

Tinubu ya ce babu dalibin da zai bar makaranta a dalilin gaza biyan kudi a mulkinsa, ya fadi haka ne a wajen taron yaye daliban jami’ar FUTO.

Asali: Legit.ng

Online view pixel