Adadin Wadanda Suka Mutu a Gaza Ya Haura 13,000, Inji Gwamnatin Hamas

Adadin Wadanda Suka Mutu a Gaza Ya Haura 13,000, Inji Gwamnatin Hamas

  • Akalla mutane 13,000 ne suka mutu sakamakon farmakin da Isra'ila ke ci gaba da kai wa kan mazauna zirin Gaza tun watan Oktoba
  • Yaki ya barke tsakanin dakarun Hamas da kuma sojojin Isra'ila kan farmakin da Hamas ta kai a ranar 7 ga watan Oktoban da ya gabata
  • Yaki tsakanin Isra'ilawa da mutanen Falasdinu ba sabo bane, hakan ya faro ne tun bayan mamayar Isra'ila a yankin Larabawa

Salisu Ibrahim kwararren editan fasaha, kudi da al'amuran yau da kullum ne, yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru takwas.

Zirin Gaza - Gwamnatin Hamas ta ta ce ya zuwa yau Lahadi adadin mutanen da suka mutu sakamakon fadan da ake gwabzawa tsakanin sojojin Isra'ila da mayakan Hamas a yankin Falasdinu ya kai 13,000.

Rikici tsakanin Isra'ila da Hamas ya fara ne tun ranar 7 ga watan Oktoba., inda mayakan Hamas suka farmaki mazauna Isra'ila, Channels Tv ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Yan ta'adda fiye da 60 sun mutu yayin da sabon yaki ya barke tsakanin Boko Haram da ISWAP

An hallaka mutane sama da 13,000 a Gaza
Yadda Isra'ila ke ci gaba da kai hari kan Gaza | Hoto: @therleez
Asali: Twitter

Bayan haka ne gwamnatin Isra'ila ta fara kai harin daukar fansa kan mazauna Gaza a nufin lallasa dakarun Hamas da ke boye a ramukan kariya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mutanen da aka akshe a Gaza

Gwamnatin Hamas ta ce sama da 5,500 ne yara daga cikin wadanda suka mutu, tare da mata 3,500, inda aka jikkata wasu mutane 30,000, India Times ta tattaro.

A baya ma’aikatar lafiya ta kasar ta ce ba za ta iya bayar da adadin adadin wadanda aka kashe ba saboda yadda aka danne gawarwaki da yawa a kasan baraguzan gine-gine.

An fara yakin Gaza da Isra'ila ne shekaru da dama, wanda hakan ya cinye rayukan mutane da yawa, musamman Falasdinawa.

An yi zabe kan tsagaita wuta a Gaza

A wani labarin, Najeriya da wasu kasashe 119 ne a ranar Juma'a suka kada kuri'ar amincewa da kudurin da ke kira da a samar da "zaman lafiya mai dorewa" tsakanin sojojin Isra'ila da Hamas a Gaza.

Kara karanta wannan

Dakarun Najeriya sun kama ’yan ta’adda 122, sun ceto mutane 189 cikin mako daya, DHQ

Har ila yau, tanasun amince da ci gaba da shigar da kayayyakin agaji da rayuwar yau da kullum a yankin na Zirin Gaza mai fama da takurar Isra'ila, rahoton Al-Jazeera.

Kudirin da kasashen Larabawa suka shirya ya samu kuri'u 120 na goyon baya, 14 na adawa da kuma 45 suka ki bayyana matsayarsu.

Asali: Legit.ng

Online view pixel