Gwamnan PDP Ya Ciri Tuta, Ya Ƙara Wa Ma'aikata da Ƴan Fansho Albashi a Jiharsa

Gwamnan PDP Ya Ciri Tuta, Ya Ƙara Wa Ma'aikata da Ƴan Fansho Albashi a Jiharsa

  • Seyi Makinde ya kara wa ma'aikata N25,000, masu karban fansho N15,000 a matsayin tallafin rage radaɗi
  • Gwamnan ya bayyana haka ne a gaban shugabannin ƙungiyoyin kwadago reshen jihar jihar a bakin shiga Ofishinsa a Ibadan
  • Wannan na zuwa ne bayan gwamnatin tarayya ta ƙara wa ma'aikata N35,000 a albashinsu domin rage radadin cire tallafin mai

Ahmad Yusuf, gogaggen Edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Oyo - Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo ya amince da biyan N25,000 ga ma'aikata da kuma N15,000 ga masu karbar fansho a matsayin kyautar albashi, The Nation ta ruwaito.

Gwamnan na jam'iyyar PDP ya ce wannan ƙarin albashin zai shafe tsawon watanni 6 kuma sakamakon haka za a samu ƙarin Naira biliyan 2.2 a tsarin albashin Oyo.

Kara karanta wannan

Wike vs Fubara: Jerin gwamnonin da suka yi nasara kan iyayen gidansu na siyasa

Gwamnan Oyo, Seyi Makinde, na jawabi ga ma'aikata.
Gwamnan PDP Ya Ciri Tuta, Ya Ƙara Wa Ma'aikata da Ƴan Fansho Albashi a Jiharsa Hoto: thenation
Asali: UGC

Makinde ya yi wannan furuci ne yayin da yake jawabi ga dandazon ma'aikata a ƙofar shiga ofishin gwamna da ke gidan gwamnatin jihar Oyo a Ibadan ranar Litinin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Manyan jiga-jigan da suka raka Makinde

Gwamnan ya samu rakiyar shugabannin ƙungiyoyin kwadago na jihar wanda suka haɗa da, Kwamared Kayode Martins (NLC), Kwamarwd Bosun Olabiyi (TUC), da Kwamared Olaonipekun Oluwaseun.

Dukkansu sun halarci wurin da Gwamna Makainde ya ambaci ƙarin tagomashi ga ma'aikata da ƴan fanshon jihar Oyo ranar Litinin, 6 ga watan Nuwamba, 2023.

Sauran kusoshin gwamnati da suka take wa Makinde baya yayin wannan jawabi sun haɗa da mai bada shawara ta musamman kan harkokin kwadago, Adebayo Titilola-Sodo, da Idowu Ogedengbe da sauransu.

Tun da farko, ma'aikatan sun mamaye ofishin mai girma gwamnan a wani ɓangare na matsayar da suka cimma wa zamansu na ranar Litinin.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Malam Dikko ta bankaɗo wasu illoli da ƴan bindiga suka yi a Jihar Katsina

Sun yi haka ne domin tabbatar da an kawo ƙarshen batun karin albashin lokaci ɗaya duba da wahalar da aka shiga tun bayan cire tallafin man fetur.

Obi ya maida martani ga hukuncin Kotun ƙoli

A wani rahoton kuma Mista Peter Obi ya caccaki hukuncin Kotun ƙoli yana mai cewa ta rusa tunanin ƴan Najeriya na samun adalci a ɓangaren shari'a

Ɗan takarar shugaban ƙasa a inuwar LP ya faɗi haka ne yayin hira da ƴan jarida a Abuja ranar Litinin, 6 ga watan Nuwamba, 2023.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262