Tinubu Ya Yi Alkawarin Inganta Rayuwar Malamai A Najeriya

Tinubu Ya Yi Alkawarin Inganta Rayuwar Malamai A Najeriya

  • Yayin da ake bikin ranar malamai ta duniya, Shugaba Tinubu ya yi alkawari ga malaman Najeriya
  • Tinubu ya yi alkawarin saka wa malamai tun a duniya ganin irin tasirin da su ke da shi wurin inganta rayuwar al'umma
  • Shugaban ya ce babu wata hanya da ke saurin sauya akalar rayuwar al'umma ta hanya mai kyau kamar ilimi

FCT, Abuja - Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya yi alkawarin saka wa malamai a irin kokarin da su ke yi na inganta harkokin ilimi.

Tinubu ya bayyana haka ne a yau Alhamis 5 ga watan Oktoba a shafinsa na Twitter.

Tinubu ya yi alkawarin inganta harkar ilimi da malaman makaranta
Tinubu Ya Yi Alkawarin Ga Malamai A Najeriya. Hoto: Bola Ahmed Tinubu.
Asali: Facebook

Wane alkawari Tinubu ya yi ga malamai?

Shugaban ya fadi haka ne yayin ya ke taya al'ummar Najeriya bikin ranar malamai ta duniya a yau Alhamis, Tribune ta tattaro.

Kara karanta wannan

Alkalai Sun Shiga Taitayinsu Yayin Da CJN Ariwoola Ya Tura Musu Muhimmin Sako Na Jan Hankali Kan Yanke Hukunci

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce babu wata hanyar tsira da ke da tasiri a rayuwar al'umma kamar ilimi a kasa.

Ya kara da cewa a karkashin mulkinsa zai bai wa malamai da harkar ilimi kulawa na musamman don inganta rayuwar al'ummar kasar.

Ya ce:

"Na yi imanin cewa babu wata mota da za ta kai ka inda ka ke so lafiya kamar harkar ilimi.
"Wannan na daga cikin dalilan da su ka sa ko wane yaro a kasar duk yadda matakinsa ya ke a rayuwa ke saka tsammanin samun damarmaki a nan gaba."

Meye Tinubu ya ce kan inganta ilimi da malamai?

Tinubu ya ce ilimi ne kadai ke sauya akalar rayuwar mutane a kankanin lokaci ba tare da tsaiko ba, cewar Vanguard.

Ya kara da cewa:

"Yayin da mu ke bikin ranar malamai ta duniya, ina mai tabbatar muku cewa gwamnatina za ta yi duk mai yiyuwa don saka wa malamai.

Kara karanta wannan

Takardun Tinubu: Minista Ya Yi Martani, Ya Tura Muhimmin Sako Ga 'Yan Najeriya

"Ilimi ne kadai ke sauya rayuwar al'umma ko iyalai cikin kankanin lokaci da al'ajabi."

A kokarin inganta rayuwar ma'aikata, Tinubu ya kara Naira dubu 35 a albashin ma'aikata don rage musu radadin cire tallafi.

Wannan na zuwa ne bayan Kungiyar Kwadago ta NLC ta yi barazanar shiga yajin aiki a wannan mako.

NLC ta yi wa ma'aikata albishir

A wani labarin, Kungiyar NLC ta yi wa ma'aikata albishir na sabon mafi karancin albashi.

Kungiyar ta ce a tattaunawar da za ta yi nan gaba za ta bukaci dubu 100 zuwa 200 mafi karancin albashi.

Asali: Legit.ng

Online view pixel