Dakarun Sojin Najeriya Sun Gano Masana'antar Kera Makamai a Jihar Kaduna
- Dakarun sojin Najeriya sun gano wata masana'antar ƙera bindigu a ƙaramar hukumar Jema'a da ke kudancin Kaduna
- Sojojin sun kama wani hatsabibin mai sayar da makamai da suka jima suna nema ruwa a jallo, sun kama wani a masana'antar
- Kwamandan rundunar Operation Save Haven ya jinjina wa dakarun sojin kana ya ce zasu kamo sauran waɗanda suka arce
DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!
Jihar Kaduna - Rundunar sojin Operation Save Haven ta bankaɗo wata masana'antar ƙera bindigogi a garin Kafanchan, ƙaramar hukumar Jema'a a jihar Kaduna.
Rundunar sojin ta samu wannan nasara ne sakamakon bin diddigi da leƙen asiri na tsawon mako ɗaya, wanda ya yi sanadin kama wani hatsabibi, Napoleon John.

Asali: Twitter
John na ɗaya daga cikin mutanen da rundunar OPSH ke nema ruwa a jallo bisa zargin hannu a tada zaune tsaye da kuma sayar da makamai a jihar Kaduna.

Kara karanta wannan
Bayan Abba Gida-Gida, Kotun Zabe Ta Ƙara Yanke Hukunci Kan Nasarar Gwamnan PDP a Arewa
Bayan ya shiga hannu, ya tabbatar da irin ɗanyen aikin da yake da hannu a ciki kana ya jagoranci dakarun soji zuwa wata masana'antar ƙera makamai.
Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!
Wannan nasara da sojojin suka samu na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da hukumar sojin Najeriya ta wallafa a shafinta na Manhajar X ranar Jumu'a, 22 ga watan Satumba.
Sojojin sun kama wani Monday Duniya a masana'antar wanda ya tabbatar da cewa ya shafe sama da shekaru biyar yana sana'ar ƙera bindiga da siyarwa a Kaduna da Filato.
Sanarwan hukumar sojin ta ce:
"Binciken da muka yi a masana’antar ya nuna wasu tarin makamai, da suka hada da, bindigogi kirar AK-47 na gida, da bindigu kirar AK-47 na soja, bindigu masu sarrafa kansu, da dai sauransu."
Kwamanda ya yaba wa dakarun soji

Kara karanta wannan
Yanzu-Yanzu: An Kammala Binciken Gawar Fitaccen Mawakin Nan Da Ka Tono Daga Ƙabari, Bayanai Sun Fito
Da yake jinjinawa sojojin, kwamandan rundunar OPSH, ya sha alwashin cewa dakaru ba zasu yi ƙasa a guiwa ba wajen kamo sauran abokan aikin 'yan ta'addan da suka arce.
Janar AE Abubakar ya kuma gode wa ɗaukacin al'umma bisa goyon bayan da su ke bai wa sojoji a yaƙin da suke yi kana ya roƙi su ci gaba da taimaka wa da bayanan sirri.
'Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa da Fasto, Ɗiyarsa da Wani Mutum Daya a Kalaba
A wani rahoton na daban 'Yan bindiga sun yi awon gaba da Malamin addinin Kirista da ɗiyarsa da wani mutum ɗaya a Kalaba, jihar Kuros Riba.
Rahotanni sun bayyana cewa maharan sun sace abin harinsu a jirgin ruwa da misalin ƙarfe 8 zuwa 9 na daren ranar Alhamis.
Asali: Legit.ng