Matsalar Tsaro: Abinda Ya Sa Iyaye Ke Fargabar Tura 'Ya'yansu Makaranta, Ministan Tinubu

Matsalar Tsaro: Abinda Ya Sa Iyaye Ke Fargabar Tura 'Ya'yansu Makaranta, Ministan Tinubu

  • Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa iyaye na tsoron tura 'ya'yansu makaranta ne saboda tsoron harin yan bindiga
  • Ministan harkokin cikin gida, Tunji-Ojo ya ce yawan hare-haren da ake kaiwa makarantu tun 2014 babban abin damuwa ne
  • Gwamnan jihar Benuwai ta tabbatar da cewa gwamnatinsa zata bada goyon baya a shirin samar da aminci a makarantun jihar

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

FCT Abuja - Ministan harkokin cikin gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, ya ce a yanzu iyaye na tsoron tura 'ya'yansu makaranta saboda matsalar tsaron da ta damu ƙasar nan.

Tunji-Ojo ya faɗi haka ne a sakonsa na fatan alheri da ya gabatar a wajen taron kaddamar da tsarin “Samar da tsaro a makarantu” da aka gudanar a Makurdi, babban birnin jihar Benuwai.

Ministan cikin gida, Tunji-Ojo.
Matsalar Tsaro: Abinda Ya Sa Iyaye Ke Fargabar Tura 'Ya'yansu Makaranta, Ministan Tinubu Hoto: dailytrust
Asali: UGC

Ya ce, "Iyaye suna tsoron tura 'ya'yansu makaranta saboda tsoron kai hare-haren 'yan ta'adda."

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu Ya Gana da Gwamnan PDP Da Tawagar Masu Ruwa da Tsakin Jiharsa a Villa

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa Ministan ya yi jawabi ne ta bakin kwamandan rundunar jami'an Sibil Difens (NSCDC), Ahmed Abubakar Audi, wanda ya wakilce shi a wurin taron.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Ministan ya jaddada cewa taɓarɓarewar tsaro da yawan kai hari makarantun ƙasar nan tun 2014 irin wanda aka sace ɗaruruwan ɗalibai mata a Chibok, ba ƙaramin abun damuwa bane.

Sai dai a nasa jawabin a wurin bikin yaye jami'ai 364 da aka ba horon samar da tsaro a makarantun Benuwai da sauran jihohi, Mista Audi ya yaba da tsarin tsaro a makarantu.

Wane nasarori sabon tsarin tabbatar da tsaro a makarantun ya samu?

Ya bayyana cewa zuwa yanzu shirin ya daƙile kai hare-hare sama da 30 a makarantun fadin kasar, tun bayan da aka fara aiwatar da shi a Najeriya, rahoton Trust Radio.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Tarayya Ta Ba Mambobin Majalisar Wakilai Tallafin N100m? Gaskiya Ta Fito Filii

Gwamna Hyacinth Alia, a jawabinsa na musamman a wajen bikin, ya yi alkawarin goyon baya daga gwamnatinsa wajen ba da fifiko kan harkokin tsaro a makarantu, inda ya jaddada muhimmiyar rawar da ilimi ke takawa wajen ci gaba.

Shugaba Tinubu Ya Sa Labule da Ganduje da Hafsoshin Tsaro a Villa

A wani rahoton kuma Bola Ahmed Tinubu ya gana da shugaban APC na ƙasa, Abdullahi Ganduje, da manyan hafsoshin tsaro a Aso Villa.

Wakilan ƙungiyar fulani makiyaya ta ƙasa MACBAN sun halarci zaman wanda ya maida hankali kan muhimmin batu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262