Ana Ta Kokarin Daukar Mataki a Kansu, Sojojin Juyin Mulki a Nijar Sun Yi Sabbin Nade-Nade

Ana Ta Kokarin Daukar Mataki a Kansu, Sojojin Juyin Mulki a Nijar Sun Yi Sabbin Nade-Nade

  • Yayin da ake kokarin kwace mulki daga hannun sojojin Nijar, sun yi sabbin nade-nade a shugabancin kasar
  • An nada ministan tsaro da kuma sauran mukamai masu muhimmanci game da tsaron kasar ta Nijar
  • Sun bayyana cewa, suna shirye da daukar duk wani kalubalen farmaki daga sojojin ECOWAS a kowane lokaci

Yamai, Nijar - Shugabannin sojin Nijar da ke rike da kasar a yanzu sun yi zabbin nade-nade a karkashin mulkinsu.

Wannan na zuwa ne yayin da suka cika kusan mako da yin juyin mulki tare da hambarar da gwamnatin Mohamed Bazoum.

A cikin wata sanarwar da suka fitar a ranar Juma'a da dare, sun bayyana nada Moussa Salau Barmou a kujerar babban hafsun hafsoshin sojin Nijar.

An i sabbin nade-nade a shugabancin sojojin Nijar
Shugaban sojin Nijar, Tchiani | Hoto: dw.com
Asali: Twitter

Yadda sauran mukamai suka kasance a sojin Nijar

Hakazalika, sanarwar ta bayyana nada Kanal Amirou Kader zai ya zama mataimakinsa, kamar yadda BBC Hausa ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Shikenan: Sanatocin Najeriya sun yi maganar karshe kan batun tura sojojin Najeriya su yaki na Nijar

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A bangare guda, Manjo Kanar Sani Kiaou ne zai kasance sabon shugaban rundunar sojin kasa a kasar.

Kanar Abdoutahamane Zakata zai rike mukamin mataimakin shugaban rundunar sojin kasan Nijar.

A bangaren ofishin ministan tsaron kasar, sanarwar ta ce an nada Janar Sani Kache don kula da wannan fannin.

A shirye muke mu tunkari sojojin ECOWAS, inji sojin Nijar

Ya zuwa yanzu, sojojin Nijar sun ce a shirye suke su tunkari duk wani kalubale na farmaki daga sojojin kungiyar ECOWAS zuwa kasarsu.

Tun bayan hambarar da gwamnatin Bazoum, sojojin Nijar suka samu gargadi daga kungiyar raya kasashen Afrika ta Yamma (ECOWAS) da bayanai masu tsauri.

Kungiyar ta yi barazanar mai da Nijar saniyar ware tare da kakaba mata takunkumin da ka iya jawo sartse ga ci gaban mulkin na soji.

Hakazalika, ECOWAS ta ce za ta yi amfani da karfin soja don tabbatar da mai da Bazoum kan mulkin Nijar.

Kara karanta wannan

Juyin Mulki: Hambararren Shugaban Nijar Bazoum Ya Aike da Sabon Saƙo Ga Amurka da Wasu Ƙasashe

Sanatocin Najeriya sun ce basu amince a tura sojin kasar su yaki na Nijar ba

Sai dai, ECOWAS ta samu tsaiko yayin da Sanatoci a Najeriya suka ce ba za su amince a tura sojin Najeriya zuwa Nijar ba.

A cewar rahoto, sama da 90% na Sanatocin ne suka bayyana rashin amincewarsu da yunkurin Shugabancin Tinubu.

Amma, majalisa ta bayyana yin Allah wadai da aikin da sojoji suka yi na kifar da mulkin Mohammed Bazoum.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.