Juyin Mulki: Jerin Matakai 7 da ECOWAS Karkashin Tinubu Ke Shirin Dauka Kan Nijar

Juyin Mulki: Jerin Matakai 7 da ECOWAS Karkashin Tinubu Ke Shirin Dauka Kan Nijar

Juyin mulkin da aka yi kwanan nan a jamhuriyar Nijar, wanda ake ganin koma baya ne ga demokuraɗiyya ya fusata ƙungiyar raya ƙasashen yammacin Afirka (ECOWAS).

Channels tv ta tattaro cewa karkashin jagorancin shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ƙungiyar ECOWAS ta amince da ɗaukar tsauraran matakai guda 7 kan jamhuriyar Nijar.

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu.
Juyin Mulki: Jerin Matakai 7 da ECOWAS Karkashin Tinubu Ke Shirin Dauka Kan Nijar Hoto: Bola Ahmed Tinubu
Asali: Facebook

A taron ta na baya-bayan nan, ECOWAS ta aminta da ɗaukar matakan a yunkurin dawo da mulkin Demokaraɗiyya a Nijar, ɗaya daga cikin mambobin ƙungiyar.

Matakan da aka ayyana, tun daga na diflomasiyya har zuwa yiwuwar sanya takunkumi, sun nuna yadda kungiyar ECOWAS ke kokarin kare mutuncin dimokradiyya a yankin.

A wannan shafin mun haɗa muku matakai bakwai da ECOWAS ta yanke shawarar ɗauka a wani yunƙuri na kawar da wannan juyin mulki da sojoji suka yi.

Kara karanta wannan

Juyin Mulki: Hambararren Shugaban Nijar Bazoum Ya Aike da Sabon Saƙo Ga Amurka da Wasu Ƙasashe

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Matakan na kunshe ne a cikin wata wasika da shugaba Tinubu ya aika majalisar dattawa ranar Juma’a, inda ya sanar da majalisar shawarar da kungiyar ECOWAS ta yanke kan halin da ake ciki a Jamhuriyar Nijar.

A cewar Tinubu, ECOWAS karkashin jagorancinsa ta yi Allah wadai da juyin mulkin gaba daya tare da kudurtan neman dawo da gwamnatin da aka zaba ta hanyar dimokradiyya.

Jerin matakai 7 da ECOWAS ta yanke shawarar ɗauka

Rahoton Daily Trust ya ce a yunkurin dawo da zaman lafiya da mulkin demokuraɗiyya, ECOWAS ta kira taro kuma ta cimma matsaya kamar haka:

1. Kulle dukkan wasu iyakoki da ƙasar Nijar tare da dawo da ayyukan motsa jikin sojoji a bakin iyakokin.

2. Katse wutar lantarƙin da ake kai wa jamhuriyar Nijar.

3. Tattara tallafin kasashen duniya domin tabbatar da an aiwatar da shawarwarin da ECOWAS ta yanke a zamanta.

Kara karanta wannan

Juyin Mulki: Hukumar Kwastam Ta Yi Bayani Kan Dalilin Rufe Iyakokin Najeriya Da Nijar

4. Hana dukkan jiragen sama shiga ko fitowa daga jamhuriyar Nijar.

5. Dakatar da kayan abincin da ke hanyar zuwa Nijar musamman daga jihar Legas da bakin teku.

6. Wayar da kan ‘yan Najeriya su san muhimmancin wadannan matakai musamman ta kafafen sada zumunta.

7. Ɗaukar matakin soji kan masu jurin mulkin idan sun yi taurin kai.

Sanatocin Arewa Ba Su Yarda Tinubu Ya Shiga Yaki da Kasar Nijar ba

A wani rahoton kuma Sanatocin da su ka fito daga jihohin Arewacin Najeriya, ba su gamsu da maganar daukar makami a kan sojojin Jamhuriyyar Nijar ba.

Wakilan jihohin Arewa a majalisar dattawa, sun fadawa Mai girma shugaban Najeriya cewa ya sake nazari kan maganar shiga Nijar da yaki.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262