Tashin Hankali Yayin da Fitaccen Fasto, Chibuzor Ya Fadi Shirim a Filin Jirgin Sama, an Zace Dashi Asibiti

Tashin Hankali Yayin da Fitaccen Fasto, Chibuzor Ya Fadi Shirim a Filin Jirgin Sama, an Zace Dashi Asibiti

  • Rahoton da muke samu ya bayyana yadda wani fitaccen malamin addinin Kirista ke cikin matsanancin halin rashin lafiya
  • Ya zuwa yanzu, an ce an kwantar dashi a wani asibiti, inda ake neman jama’a su sanya shi a addu’ar Allah ya bashi lafiya
  • Ba a bayyana zahirin abin da ya faru dashi ba, amma ana fargabar rashin lafiya ne da ya kai ga kwnatar dashi nan take

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Najeriya - A ranar Juma’ar da ta gabata ne faston da ya kafa cocin Omega Power Ministries, Chibuzor Gift Chinyere ya fadi shirim a wani filin jirgin saman da a bayyana ba saboda wani ciwon da ake fargabar na damunsa.

Malamin na coci ya shiga tereren kafafen yada labarai a shekarun baya yayin da ya dauki wasu yara ma’aikatan gidan cin abinci ya tura su karatu kasar waje.

Kara karanta wannan

Mutane 6 Sun Rasu a Borno Yayin Da Wani Bam Da 'Yan Boko Haram Suka Binne a Kan Hanya Ya Tashi

A baya-bayan nan, ya bayyana daukar nauyin iyayen wata dalibar da aka kashe a Sokoto bisa zarginta da cin mutuncin manzon tsira; Annabi Muhammadu SAW.

Babban malamin coci ya fadi a filin jirgin sama
Yadda malamin coci ya fadi a filin jirgin sama | Hoto: Omega Power Ministry
Asali: Facebook

Sai dai, an yi ta korafe-korafe kan cewa, kyautar da ya yi alkawarin yiwa iyayen Deborah ta samu cikas, inda daga baya ya karyata hakan.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An ga faston a kwance a kasa a filin jirgin sama

A wani hoton da ya yadu a kafar sada zumunta, an ga lokacin da faston ke kwance a kasa kafin daga bisani aka tattara shi zuwa asibiti.

A bidiyon da aka yada a Facebook, an ce malamin dan asalin jihar jihar Ribas tabbas baya cikin hayyacinsa a filin jirgin saman.

Sakon da aka wallafa hade da bidiyon ya ce:

“Mu kokarta don Allah mu sanya Ubanmu a cikin addu’o’inmu.”

A bangare guda, mabiya mashabar da magoya baya malamin na ci gaba da zabga addu’o’i a kafafen sada zumunta.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Tinubu Ta Kirkiro Sabuwar Hanyar Tatsar Kudi Daga Masu Hawa Titi

Fasto ya ba iyayen Deborah gida

A wani labarin, Chibuzor Chinyere, babban faston cocin Omega Power Ministry, (OPM), ya mika kyautan gida da mota ga iyalan Deborah Samuel Yakubu, dalibar da aka kashe a Sokoto kan batanci ga Annabi (SAW), The Cable ta rahoto.

An yi wa Deborah, dalibar aji na 2 a Kwalejin Ilmi ta Shehu Shagari a Sokoto duka da sanduna kafin nan aka cinna mata wuta a harabar makarantar a ranar 12 ga watan Mayu.

Duk da cewa wasu sun yi tir da kisar da aka yi mata a Najeriya da kasashen ketare, an yi zanga-zanga a Sokoto na neman ganin an sako wadanda ake zargi da hannu a kisar ta.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.