Mutum 24 Sun Mutu Yayin Da Wata Babban Mota Da Ta Tashi Daga Zaria Zuwa Legas Ta Yi Haɗari

Mutum 24 Sun Mutu Yayin Da Wata Babban Mota Da Ta Tashi Daga Zaria Zuwa Legas Ta Yi Haɗari

  • Wani mummunan hadarin mota ya yi sanadin salwantar rayukan mutane 24 a Jihar Niger
  • Hadarin da ya auku da daren Litinin da ya rutsa da wata babbar motar daukar kaya dauke da fasinja daga Zaria zuwa Lagos dauke da mutane 87
  • Hukumar kiyaye hadura ta kasa ta tabbatar da faruwar lamarin tare da shaida cewa an kwashe wanda su ka jikkata zuwa asibiti yayin da aka ajiye gawarwakin a dakin adana gawa na Kutigi

Jihar Niger - Wani hadarin mota ya yi sanadin salwantar rayuka 24 da daren Litinin 27 ga watan Maris a karamar hukumar Lavun da ke Jihar Niger, rahoton The Punch.

Babban motar da ke dauke da fasinjojin tana kan hanyarta na zuwa Legas ne daga Zaria kuma akwai mutane 87 a cikinta.

Hukumar FRSC
Rayyuka 24 sun salwanta a hadarin mota a jihar Neja. Hoto: The Punch
Asali: Facebook

Kara karanta wannan

A shirye nake: Zababben gwamnan Katsina ya fadi abin da zai a ranar da ya karbi mulki

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Babban kwamandan shiyya na Jihar Niger a Hukumar Kiyaye Hadura ta Kasa, FRSC, Kumar Tsukwan, shi ne ya bayyana haka a rahoton masaniyar farko na hadari ya kuma bawa wakilin majiyarmu, hadarin ya faru a kauyen Etsu Woro.

''Fasinja 24 da ke tahowa daga Zaria zuwa Lagos sun mutu a hadarin da ya hada da babbar mota dauke da fasinja 87 a kauyen Etsu Woro da ke karamar hukumar Lavun a Jihar Niger," in ji shi.

Adadin mutanen da ke cikin motar

Tsukwan ya ce akwai maza 17, mata hudu da kananan yara 4 sun mutu a babbar motar Lone Sino a hadarin tare da karin 45 da su ka ji rauni daban-daban aka garzaya da su asibiti don karbar magani.

Ya kara da cewa an kai gawarwakin zuwa dakin ajiye gawa.

Kara karanta wannan

A kalla Rayuka 11 ne Suka Salwanta a Wasu Hadururruka Daban-Daban a Niger

Ya ce:

''An kwashe wanda abin ya shafa daga wajen da hadarin ya faru zuwa babban asibitin Kutigi don karbar magani yayin da aka ajiye gawarwakin a dakin adana gawa na Kutigi.''

Hatsarin mota ya yi sanadin rasa rayyuka biyu a jihar Jigawa

A wani rahoton mai kama da wannan kun ji cewa wasu mutane biyu sun rasu a wani hadarin mota da ya afkuw a hanyar Jahun zuwa Kiyawa a Jihar Jigawa.

Adamu Shehu, mai magana da yawun hukumar tsaro ta NSCDC na jihar Jigawa ya tabbatar da hakan a ranar Juma'a.

Asali: Legit.ng

Online view pixel