Allah Ya Yiwa Daya Daga Cikin ’Yan Majalisun Imo, Arthur Egwim Rasuwa Jiya Litinin

Allah Ya Yiwa Daya Daga Cikin ’Yan Majalisun Imo, Arthur Egwim Rasuwa Jiya Litinin

  • An samu mummunan labarin rasuwar dan majalisar wakilai a jihar Imo bayan wata jinya da ya yi a kasar waje
  • Rahoto ya bayyana kadan daga tarihin aikinsa da kuma gwagwarmayarsa ta siyasa tun daga 2015 zuwa yanzu
  • Majiya ta ba da labarin yadda aka tallafa wajen kai shi kasar waje domin yi masa jinya, amma bai tsira daga cutar ba

Jihar Imo - Daya daga cikin fitattun ‘yan majalisar dokokin jihar Imo, Hon. Arthur Egwim ya kwanta dama, rahoton jaridar The Nation.

Dan majalisar da ya fito daga yankin Orlu ya rasu ne a jiya Litinin 27 ga watan Maris bayan jinyar cutar daji.

An zabe shi ne a karon farko zuwa majalisar a karkashin inuwar jam’iyyar APC a 2015, inda ya sake samun damar shiga majalisar a 2019 a karkashin inuwar jam’iyyar AA.

Kara karanta wannan

Dani za a yi: Tsohon gwamnan jihar Arewa ya shiga jerin masu neman kujerar shugaban majalisar dattawa

Yadda dan majalisa ya rasu a Imo
Majalisar dokokin jihar Imo | Hoto: thenationlineng.net
Asali: UGC

Mukaman da ya rike a majalisa

Ya kasancewa shugaban kwamitin kudi da asusun gwamnatin jihar a majalisar dokokin ta Imo.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hakazalika, ya kasance shugaban kwamitin harkar masarautu da harkokin al’umma , hakazalika shugaban kwamitin shari’a a majalisar.

Arthur Egwim ya kasance dan takarar majalisar tarayya a karkashin inuwar jam’iyyar APGA a mazabar Ideato a zaben 2023.

Sai dai, ya fadi a zabe, inda dan takarar jam’iyyar PDP, Ugochinyere Imo ya lashe zaben da aka gudanar a ranar 25 ga watan Faburairu.

Yadda aka kai shi kasar waje jinya

A cewar wata majiya daga jaridar The Street Journal, dan majalisar ya kasance a kasar waje na wani dan lokaci yana jinya kafin daga bisani rai ya yi halinsa.

A cewar majiyar:

“An shilla dashi kasar waje don yi masa aiki amma bai tsira ba. Gwamnatin jihar ce ta tallafa masa wajen neman magani a kasar waje. Tabbas abin jimami ne.

Kara karanta wannan

Za ku sha mamaki: Sabon gwamnan wata jiha ya fadi yadda zai ji da albashin ma'aikata a jihar

“Ya kasance dan majalisa mai kokari kuma mai mutunta kowa, daidai lokacin da yake kokarin mika wa zababben dan majalisa a watan Yuni, ya tafi.”

A jihar ta Imo cikin makon nan aka kashe wasu jami'an tsaron hukumar NSCDC a lokacin da suka bakin aiki.

A cewar rahoto, baya ga kashe jami'ai uku, an kuma hallaka wasu fararen hula biyu da ke wucewa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.