IPOB Ta Shiga Jerin Kungiyoyin Yan Ta'adda 10 Mafi Hatsari a Duniya

IPOB Ta Shiga Jerin Kungiyoyin Yan Ta'adda 10 Mafi Hatsari a Duniya

Rahoton ta'addanci na duniya (GTI) ya sanya IPOB a cikin jerin ƙungiyoyin yan ta'addda 20 masu haɗari a duniya.

Ƙungiyar masu fafutukar kafa ƙasar Biafara (IPOB) ta kai matsayi na 10 a cikin jerin ƙungiyoyin 'yan ta'adda mafi haɗari a faɗin duniya.

Shugaban IPOB, Nnamdi Kanu.
DSS sun raka shugaban IPOB zuwa wajen Kotun tarayya Hoto: Kola Sulaiman/AFP
Asali: UGC

Makarantar tattalin arziki da kuma bin diddigin ayyukan ta'addanci a duniya ce take wallafa rahoton GTI. A sabon rahoton da ta fitar ranar Talata 14 ga watan Maris, IPOB na matsayi na 10.

Jerin ƙungiyoyin 'yan ta'adda 20 mafi hatsari a duniya

MatsayiSunan kungiyaAdadin kisaHare-hareYawan masu rauni
1IS1045410644
2Al-shabaab7843151016
3IS ta lardin Khorasan498141132
4Jama'atu Nusrat Islam (JNIM)27977215
5Balochistan Liberation Army (BLA)23330113
6Islamic State West Africa (ISWAP)21965118
7Boko Haram2046451
8Taliban ta Pakistan13790187
10Yan awaren IPOB574016
11Kurdistan Workers Party (PƘK)4054150
12Communist Party a Indiya396130
13Al-Qaeda ta yankin larabawa (AQAP)17623
14FARC ta ƙasar Colombia161737
15New Peoples Army (NPA)191325
16Ƙungiyar LeT8638
17Balochistan Liberation Front (BLF) 648
18National Liberation Army (ELN)52877
19Islamic Jihad5210
20Belochistan Republic Army418

Kara karanta wannan

Da Dumi-Dumi: Ana Dab Da Zabe, 'Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Sakataren APC a Jihar Rivers

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

IPOB ta kafa tarihin a shekarar 2022 - GTI

A cewar rahoton aikata ta'addanci na duniya (GTI), ƙungiyar IPOB ta kaddamar da hare-hare da kashe-kashe mafi yawa a tarihinta a shekarar 2022.

"Kungiyar IPOB, wacce gwamnatin Najeriya ta ayyana a matsayin ƙungiyar ta'addanci ta aikata ta'asa mafi muni a 2022. Su ke da alhakin kai hare-hare 40 da kisan 57 a 2022."

"Hakan ya nuna an samu karin hare-hare 26 da kisan mutane 34 idan aka kwatanta da shekarar da ta gabaci 2022," inji rahoton.

A wani labarin kuma Najeriya ta koma matsayi na 36 a jerin kasashe masu karfin sojoji 145 na faɗin duniya

A sabon rahoton da aka fitar, Najeriya ta samu koma baya da matsayi ɗaya, daga matsayi na 35 zuwa matsayi na 36 a duniya.

Kara karanta wannan

Jerin Mata 24 Da Ke Takarar Kujerar Gwamna a Zaben Ranar Asabar

Haka zalika a jerin kasahen nahiyar Afirka, Najeriya ta sake matsawa baya da matsayi ɗaya a sabon rahoton.

Asali: Legit.ng

Online view pixel