Zaben Gwamnoni: Jerin Mata 24 Da Ke Neman Takara a Fadin Jihohin Najeriya

Zaben Gwamnoni: Jerin Mata 24 Da Ke Neman Takara a Fadin Jihohin Najeriya

Za a gudanar da zaben gwamnoni a fadin jihohi 28 cikin 36 da ke Najeriya a ranar Asabar, 18 ga watan Maris. Akalla mata guda 24 ne za su fafata da takwarorinsu maza wajen neman kujerun gwamnoni a sassa daban-daban na kasar.

Legit.ng ta lura cewa yawan mata masu shiga harkar siyasa na kara karuwa a Najeriya musamman ma a zaben 2023.

Jam’iyyun siyasa 18 ne za su gabatar da yan takara a zaben amma mata biyu ne kawai suka lashe tikitin manyan jam’iyyun siyasa uku da suka hada APC mai mulki, babbar jam’iyyar adawa ta PDP da kuma sabuwar jam’iyyar matasa ta Labour Party, Premium Times ta rahoto.

Wasu daga cikin mata masu takarar gwamna
Zaben Gwamnoni: Jerin Mata 24 Da Ke Neman Takara a Fadin Jihohin Najeriya Hoto: BBC
Asali: UGC

Sai dai wacce ta fi shahara cikin yan takara 24 mata da ke neman kujerar gwamna a ranar Asabar ita ce Aishatu Dahiru Binani, wacce ke rike da tutar APC a jihar Adamawa.

Ga cikakkun jerin mata 24 da ke neman kujerar gwamna a zaben

  1. Aishatu Dahiru Binani – APC a jihar Adamawa
  2. Gladys Johnson-Ogbuneke - SDP a jihar Abia
  3. Lancaster Okoro – PRP a jihar Abia
  4. Ekanem Abasiekeme - AA a jihar Akwa Ibom
  5. Udoh Emem Monday - SDP. a jihar Akwa Ibom
  6. Roseline Chenge - ADP a jihar Benue
  7. Aondona Dabo-Adzuana - ZLP a jihar Benue
  8. Abubakar Fatima - ADP a jihar Borno
  9. Ibiang Marikana Stanley - ADP a Cross River
  10. Onokiti Helen Agboola - Accord a jihar Delta
  11. Cosmas Annabel – APP a jihar Delta
  12. Chinenye Igwe - APM a jihar Ebonyi
  13. Ogochukwu Nweze - SDP a jihar Enugu
  14. Umar Binta Yahaya - AA a jihar Jigawa
  15. Yakubu Furera Ahmad - BP a jihar Kano
  16. Mahmud Aisha – NRM a jihar Kano
  17. Motunrayo Jaiyeola – APM a jihar Kwara
  18. Funmilayo Kupoliyi - APM a jihar Lagas
  19. Roseline Adeyemi - APP a jihar Lagas
  20. Patricia Tsakpa - ADP a jihar Nasarawa
  21. Khadijah Abdullahi-Iya - APGA a jihar Neja
  22. Aduragbemi Euba - YPP a jihar Oyo
  23. Beatrice Itubo - LP a jihar Rivers
  24. Hadiza Usman - ZLP a jihar Zamfara.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Jerin jihohi 15 da PDP ka iya lashewa a zaben gwamnoni na 2023

A wani labarin kuma, mun kawo cewa hasashe sun nuna cewa jam'iyyar PDP mai adawa a kasar ka iya nasara wajen kaso kujeru 15 a zaben gwamnoni da za a yi a ranar Asabar.

Asali: Legit.ng

Online view pixel