Wasu Kasurguman ’Yan Bindiga Sun Farmaki Gidan Talabijin da Rediyo a Jihar Ribas

Wasu Kasurguman ’Yan Bindiga Sun Farmaki Gidan Talabijin da Rediyo a Jihar Ribas

  • Wasu gungun ‘yan ta’adda sun kai farmaki kan gidan talabijin da rediyo a jihar Ribas da ke kudancin Najeriya
  • Wannan lamari ya faru ne a ranar Talata 21 ga watan Faburairun 2023 yayin da ake shirin babban zaben kasar
  • Ba wannan ne karon farko da ‘yan ta’adda ke kai farmaki kan wuraren ayyukan halas da na gwamnati ba a yankin Kudu

Jihar Ribas - Wasu ‘yan ta’adda sun kai farmaki kan wani gidan talabijin a birnin Fatakwal na jihar Ribas da ke kudancin Najeriya, rahoton Channels Tv.

Rahoton da muke samu daga gidan talabijin na Channels ya bayyana cewa, an farmaki gidan yada labaran Atlantic Tv da Wish 99.5 FM da ke Ozuoba da nakiya.

A cewar rahoton, lamarin ya faru ne da bisalin karfe 8:45 na daren ranar Talata, 21 ga watan Faburairu.

Kara karanta wannan

Da Dumi-Dumi: Bam Ya Tashi a Sakatariyar Karamar Hukuma a Arewacin Najeriya

'Yan bindiga sun yi barna a gidan talabijin a jihar Rivers
Tasiwarar jihar Ribas, jihar da ke yawan samun farmakin 'yan ta'adda | Hoto: channelstv.com
Asali: Depositphotos

Mai gidan yada labarai ya magantu

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Da yake tabbatar da faruwar lamarin ta wayar tarho ga majiya, mai gidan yada labaran, Chinyere Igwe, wanda kuma dan majalisar wakilai ne ya ce an lalata dakin janareta a harin.

A cewarsa:

“Mun sanar da ‘yan sanda, wani sashe na ‘yan sanda ya zo kuma DPO ya kira ni a yau ya ce wasu kwararru kan ilimin nakiya za su zo su fadada bincike.”

Ya zuwa yanzu dai rundunar ‘yan sanda bata yi martani kan lamarin ba, domin kuwa ba samu jin ta bakin kakakin rundunar jihar ba, Grace Iringe-Koko, rahoton Leadership.

Ya zuwa yanzu dai, an yi nasara ba a samu rasa rai a harin ba, hakazalika babu wani wanda ya samu rauni daga cikin wadanda ke cikin gidan yada labaran.

Ana yawan samun hare-haren ‘yan ta’adda a yankunan Kudancin kasar nan, musamman daga ‘yan awaren IPOB.

Kara karanta wannan

Gaskiya ta fito: Sarki Sanusi ya tona asirin abin da aka kitsa wajen sauya fasalin Naira

‘Yan bindiga sun farmaki ofishin ‘yan sanda a Anambra

A wani labarin kuma, kun ji yadda ‘yan sanda suka hallaka wasu ‘yan bindiga a wani harin da suka kai a jihar Anambra da ke Kudu maso Gabashin Najeriya.

Rahoton da muke samu ya bayyana cewa, akalla ‘yan bindiga uku ne suka mutu, kuma an kwato makamai da kayan aikata laifi.

A gefe guda, an hallaka wasu jami’ain ‘yan sanda da ke kan aiki a lokacin da tsagerun suka tsara kone ofishin yanki na ‘yan sanda.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.