Kungiyar Malaman Jami’a Ta ASUU Ba Za Ta Sake Tsundumawa Sabon Yajin Aiki Ba

Kungiyar Malaman Jami’a Ta ASUU Ba Za Ta Sake Tsundumawa Sabon Yajin Aiki Ba

  • Kungiyar malaman jami'a ta ce ba za ta kuma komawa sabon yajin aiki ba duk da gwamnati ta saba alkawarin da ta dauka musu
  • Gwamnatin Najeriya ta biya ASUU albashin rabin wata bayan da ta janye yajin aikin watanni takwas da ta shiga a watan Fabrairu
  • Kungiyar ta yi zama, ta kuma yi Allah-wadai da abin da gwamnatin Najeriya ta yi mata a makon da ya gabata

FCT, Abuja - Kungiyar malaman ta ASUU ta kammala zamanta na majalisar zartaswa, inda ta yanke ba za ta sake shiga wani sabon yajin aiki ba a nan kusa, Leadership ta ruwaito.

Sai dai, kungiyar ta yi Allah wadai da yunkurin gwamnatin tarayya na son sake tunzura mambbointa ta hanyar biyansu rabin albashi na watan Agusta.

Kara karanta wannan

Bacin rana: Kotu ta daure mai gadi a jihar Arewa bisa laifin barci a bakin aiki

A wata sanarwa da kungiyar ta fitar ranar Talata bayan kammala zaman NEC, shugaban ASUU na kasa, Farfesa Emmanuel Osodeke ya ce, malaman jami'a masu ilimi ne ba wai ma'aikata gama gari ba.

Shugabannin ASUU sun ce ba za a koma sabon yajin aiki ba
Kungiyar Malaman Jami’a Ta ASUU Ba Za Ta Sake Tsundumawa Sabon Yajin Aiki Ba | Hoto: leadership.ng
Asali: Facebook

Mun janye yajin aiki ne saboda 'yan Najeriya, inji ASUU

Ya kuma bayyana cewa, kungiyar ta janye yajin aiki a ranar 14 ga watan Oktoba ne bisa umarnin kotu da kuma yadda wasu 'yan Najeriya masu kishi suka sanya baki.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Daga cikin wadanda suka sanya baki a lamarin dawowar ASUU bakin aiki akwai shugaban majalisar wakilai, Rt. Hon. Femi Gbajabiamila.

Osodeke ya kuma bayyana cewa, kungiyar ta nuna karimci wajen bin umarnin kotu da kuma sanya bukatun 'yan Najeriya a saman komai ta hanyar komawa bakin aiki.

A bangare guda, kungiyar ta nemi goyon bayan 'yan Najeriya a kokarinta na tabbatar da an warware dukkan wata dambarwa da ke tattare da yajin aikin na malaman jami'a, kamar yadda Punch ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Albashin Rabin Wata: Majalisar Zartarwar ASUU ta Shiga Ganawar Sirri

An biya malaman jami'a rabin albashin Oktoba

Idan baku manta ba, a baya gwamnati ta biya malaman jami'a albashin watan Oktoba, amma ba su iya samun cikakken albashin ba.

Kungiyar ta bayyana fushi yayin da mambobinta suka ga rabin albashin da suke samu sabanin cikakken kamar yadda suka saba.

Wannan ya biyo bayan janye yajin ne da kungiyar ta yi a tsakiyar wata, lamarin da yasa gwamnati ta ce ba za ta biya cikakken albashi ga ASUU ba.

Asali: Legit.ng

Online view pixel