Legas: Yadda Nayi Basaja, 'Dan Sanda Ya Nemi Cin Hanci Daga Wurina a Kan Titi, PPRO

Legas: Yadda Nayi Basaja, 'Dan Sanda Ya Nemi Cin Hanci Daga Wurina a Kan Titi, PPRO

  • Kakakin rundunar 'yan sandan jihar Legas, Benjamin Hundeyin, ya sanar da abinda ya fuskanta a kan titin Legas daga 'yan sanda bayan yayi basaja
  • Hundeyin yace akwai inda yaje ko tambayarsa takardun mota ba a yi ba, yayin da ake neman ya bada cin hanci amma ya ki
  • Ya sanar da cewa babu 'dan sandan da ya gane shi duk da bai bayyana kansa ba, amma ya ga halayyar 'yan sanda a kan titi

Legas - Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Legas, Benjamin Hundeyin, ya gudanar da wani gwaji na zamantakewar al’umma inda ya yi shigar farar hula tare da tuka mota da misalin karfe 11:50 na dare kuma ya wuce ta shingayen binciken ‘yan sanda.

Hundeyin ya ce ya wuce shingayen binciken farko da na biyu, ya kara da cewa "ba a ma nemi takardunsa ba."

Kara karanta wannan

‘Yan damfara Sun yi wa Asusun Bayin Allah Tas a Banki, Sun Sace Naira Miliyan 523

Benjamin Hundeyin
Legas: Yadda Nayi Basaja, 'Dan Sanda Ya Nemi Cin Hanci Daga Wurina a Kan Titi, PPRO. Hoto daga punchng.com
Asali: UGC

Hundeyin ya yi kokarin jaddada amfanin hulda da ‘yan sanda a kan hanya cikin ladabi, yana mai cewa “girma bayarwa kake yi sannan ka samu”.

Ya kara da cewa, bai dace mutane su rika masifa ba, domin ya wuce ta wani shingen bincike bayan sun yi murmushi.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Hundeyin yayi wannan bayanin ne ta shafinsa na Twitter a yammacin ranar Alhamis, inda ya bayyana cewa jami’an ‘yan sanda sun nemi ya ba su “wani abu.”

Ya wallafa a shafinsa na twitter cewa:

“A karshe na yi gwajin zamantakewa na. Na zagaya Ikeja da misalin karfe 11:50 na dare, a cikin kayan gida cikin wata motata. Na wuce ta wurin 'yan sanda biyu. Na yi dakika biyar a wurin na farkon ba tare da yace uffan ba,kawai ya daga min hannu.
“Na shafe dakika talatin a karo na biyu.

Kara karanta wannan

Jigon PDP Ya Kara Ja Da Baya da Atiku, Yace Babu Tabbas a Kan ‘Dan Takaransu

Jami'i: Motar haya ce?

Ni: A'a. Motata ce.

Jami'i: Nemo mini wani abu mana.

Ni: Ba ni da wani abu.

Jami'i: Duba yadda kake gwanin sha'awa, nemo mani wani abu mana.

Ni: (shiru).

Jami'i: tafi.

“A lokuta biyun, ana tsayar da ni, na kunna fitilar gaba na rage gilashin da ke gefena. Ni ke fara gaisuwa. Bugu da ƙari, a karo na biyu, na yi murmushi kuma na bayyana da walwala da gangan.
“A lura: Ba su gane ni ba; nima ban bayyana kaina ba. Bai kai nan wuri ba ba. Ba a nemi takardun mota ba. Na tabbata akwai mutane da yawa da suka fuskanci irin hakan. Daban-daban bugun jini ga mutane daban-daban, na sani. Abu daya tabbata, duk da haka.
“Mutunta juna ne. Godiya ga waɗanda suka tsaya a can duk dare da rana don ƙaramin albashi. Kada ku zama masu tawali'u. Kada ku zama masu tayar da hankali ba dole ba."

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: Wani Gwamnan Arewa Ya Kamu da Rashin Lafiya, An Masa Tiyata

Falana Yayi wa FPRO Martani, Yace Shekaru 25 a Gidan Maza ne Hukunci 'Dan Sandan Da ya Mari Farar Hula

A wani labari na daban, Lauya mai rajin kare hakkin 'dan Adam kuma Babban Lauyan Najeriya, Femi Falana, ya caccaki mai magana da yawun rundunar 'yan sandan Najeriya, Olumuyiwa Adejobi kan tsokacinsa na yadda 'yan Najeriya ya dace su yi martani idan 'yan sanda sun ci zarafinsu.

Adejobe ya janyo cece-kuce a ranar Asabar yayin da yace 'yan Najeriya basu da damar yin martani inda 'yan sanda sun ci zarafinsu, Channels TV ta rahoto.

Asali: Legit.ng

Online view pixel