Yanzu-Yanzu: Fitaccen Dan Siyasan Arewa Ya Mutu A Hatsarin Mota

Yanzu-Yanzu: Fitaccen Dan Siyasan Arewa Ya Mutu A Hatsarin Mota

  • Allah ya yi wa kwamishinan matasa da wasanni na Jihar Yobe, Honarabul Goni Bukar Lawan wanda aka fi sani da BUGON rasuwa
  • Tsohon dan majalisar tarayyar ya rasu ne sakamakon hatsarin mota da ya ritsa da shi a hanyar Damaturu zuwa Kano a daren ranar Talata 2 ga watan Agusta
  • Rahotanni sun bayyana cewa mamacin ya hallarci wata jana'iza ne a garin Damaturu a ranar Talatar amma shima Allah ya masa rasuwa a hanyarsa na tafiya

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

Jihar Yobe - Kwamishinan Matasa Da Wasanni na Jihar Yobe, Hon. Goni Bukar Lawan, (BUGON) ya mutu a hatsarin mota kan hanyar Damaturu zuwa Kano.

Goni Bukar, tsohon dan majalisar wakilai na tarayya, wanda aka fi sani da BUGOM, ya rasu a daren yau Talata a hanyarsa na zuwa Jihar Kano, Leadership ta rahoto.

Kara karanta wannan

Da Ɗumi-Dumi: Tsohon Shugaban Jami'ar LASU, Farfesa Hussein, Ya Rasu

Jihar Yobe.
Fitaccen Dan Siyasan Arewa Ya Mutu A Hatsarin Mota. Hoto: @MobilePunch.
Asali: Facebook

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Jaridar ta ambaci majiya na cewa mamacin ya hallarci jana'iza a Damaturu babban birnin Jihar Yobe a yammacin ranar Talata, kafin ya kama hanyar zuwa Jihar Kano.

Za a yi jana'izarsa a ranar Laraba a Damaturu domin an koma da gawarsa Damaturu babban birnin jihar Yobe a daren ranar Talata, Daily Indepedent ita ma ta rahoto.

Ya rasu ya bar mata biyu da yara.

Allah Ya Yi Wa Tsohon Shugaban Rikon Kwarya Na BUK Rasuwa

A wani rahoton, tsohon shugaban rikon kwarya na Jami'ar Bayero ta Kano, BUK, Farfesa Danjuma Maiwada, ya rasu yana da shekaru 70 a duniya, Daily Trust ta ruwaito.

Maiwada, wanda ya yi aiki na kankanin lokaci a matsayin shugaban riko na BUK a 2004, dan asalin Jihar Katsina ne amma mafi rayuwarsa a Kano ne inda ya ke koyarwa a jami'ar tun 1976 a tsangayar ilimi.

Kara karanta wannan

Tinubu, Dangote, Gwamnoni Da Sauran Manyan Masu Fada Aji Da Suka Halarci Auren Diyar Shettima

A shekarar 2015, ya yi aiki a matsayin shugaban riko na jami'an Northwest University, Kano da yanzu ake kira Jami'ar Yusuf Maitama Sule.

Yana daga cikin masu fada a ji a tsangayar koyar da manya da ilimin addinin musulunci kuma ya koyar da malamai ciki har da shugaban jami'an na yanzu, Farfesa Sagir Adamu Abbas.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164