Ma'aikatan INEC Sun Rufe Kwamishina a Ofishinsa Saboda Rashin Biyansu Hakokinsu

Ma'aikatan INEC Sun Rufe Kwamishina a Ofishinsa Saboda Rashin Biyansu Hakokinsu

  • Ma'aikatan zabe a Jihar Abia sunyi zanga-zanga har sun rufe kwamishinan INEC na jihar a ofishinsa saboda hakokinsu
  • Daya daga cikin masu zanga-zangan da ya nemi a boye sunansa ya ce cikin kudaden har da na zaben fidda gwani na jam'iyyu da aka yi a baya-bayan nan
  • Kakakin INEC na jihar, Mr Bamidele Oyetunji ya ce matsala ne na cikin gida, kuma an warware matsalar

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

Jihar Abia - Ma'aikatan hukumar zabe mai zaman kanta, INEC, reshen Jihar Abia sun rufe kwamishinan INEC, mai kula da jihar, Joseph Iloh, a ofishinsa kan rashin biyansu hakokinsu.

Masu zanga-zangar, a ranar Talata, sun tare kofa fita daga hedkwatar INEC da ke kallon Babban Bankin Najeriya na Umuahia a ranar Talata, rahoton Vanguard.

Hukumar INEC.
Ma'aikatan INEC Sun Rufe Kwamishina a Ofishinsa Saboda Rashin Biyansu Hakokinsu. Hoto: @VanguardNGA.
Asali: UGC

Sunyi amfani da babban motarsu na ma'aikata sun rufe kofar hedkwatar suna mai cewa Kwamishinan ba zai bar ofishinsa ba zai ya biya su dukkan hakokinsu.

Kara karanta wannan

Garin neman kiba: Banki ya fece da kudin kwastomomi garin neman rancen miliyoyi

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Kwamishinan zai yi ritaya daga aiki nan da yan makonni.

A cewar daya daga cikin masu zanga-zangar da ya nemi a boye sunansa, ya ce wasu daga cikin hakokinsu har da kudin zaben fidda gwani na jam'iyyun siyasa da aka kammala a baya-bayan nan.

An yi kokarin ji ta bakin kwamishinan game da afkuwar lamarin amma ba a same shi ba a lokacin hada wannan rahoton.

Martanin hukumar INEC ta Abia

Jami'an hulda da jama'a na INEC a jihar, Mr Bamidele Oyetunji ya ce matsala ne na cikin gida, kuma an warware matsalar.

Zaben 2023: Ba Zan Yi Wa INEC Katsalandan Ba, In Ji Buhari

A wani rahoton, Shugaba Muhammadu Buhari ya sake jadada cewa gwamnatinsa za ta tabbatar Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta, INEC, ta yi zabe na adalci kuma cikin zaman lafiya a 2023.

Kara karanta wannan

Abin na yi ne: Za a dauki mutane miliyan 1 aiki a 2023 domin gano yawan 'Yan Najeriya

Ya bada tabbacin cewa ba zai yi wa INEC katsalandan ba, yana mai cewa bayan kammala zaben cikin gida na jam'iyyu, yanzu an sa ido ne kan zaben 2023 a Najeriya.

Buhari, a cewar sanarwar da kakakinsa Garba Shehu ya fitar a shafinsa na Twitter, ya yi magana ne a daren ranar Laraba a Lisbon yayin ganawarsa da yan Najeriya da ke zaune a Portugal.

Asali: Legit.ng

Online view pixel