Duk a cikin aiki ne: Jami'an kwana-kwana sun ceto zakaran da ya fada rijiya

Duk a cikin aiki ne: Jami'an kwana-kwana sun ceto zakaran da ya fada rijiya

  • Jami'an hukumar kwana-kwana sun yi nasarar ceto wani Zakara mai shekara da ya fada a cikin rijiya a unguwar Kwalli da ke birnin jihar Kano
  • Kakakin hukumar, Saminu Yusuf Abdullahi, ya bayyana cewa jami'ansu sun ceto Zakaran ne bayan sun samu kirar gaggawa daga mazauna unguwar
  • Ya ja hankalin jama’ar jihar da su guji barin rijiyoyi a bude domin gudun faruwar makamancin hakan

Kano - Jami’an hukumar kashe gobara ta Kano ta yi nasarar ceto wani zakara mai shekara daya bayan ya fada wata rijiya a unguwar Kwalli da ke birnin jihar.

Mai magana da yawun hukumar, Saminu Yusuf Abdullahi, shine ya tabbatar da hakan a gari Kano, yana mai cewa sun samu kira daga mazauna unguwar inda suka gaggauta amsa kiran tare da ceto zakaran da ransa, jaridar Aminiya ta rahoto.

Kara karanta wannan

Karin bayani: 'Yan bindiga sun kashe shugaban jam'iyyar APC a yankin Kaduna

Duk a cikin aiki ne: Jami'an kwana-kwana sun ceto zakaran da ya fada rijiya
Duk a cikin aiki ne: Jami'an kwana-kwana sun ceto zakaran da ya fada rijiya Hoto: Aminiya
Asali: UGC

Abdullahi ya ce:

“Mun samu kiran gaggawa daga wani mutum mai suna Kamalu Garba da misalin karfe 10:12 na safe, inda ya sanar da mu afkuwar lamarin.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

“Nan da nan jami’anmu suka isa wajen, sai suka tarar da wani zakara mai kimanin shekara daya ya fada a rijiya. Daga baya mun yi nasarar ceto shi cikin koshin lafiya.”

Rahoton ya kuma bayyana cewa tuni aka mika zakaran ga mamallakinsa mai suna Abdullahi Umar.

Kakakin hukumar gobarar ya kuma yi kira ga jama’ar jihar da su guji barin rijiyoyi a bude domin gudun faruwar makamancin hakan.

Wani Bawan Allah Mai Shekaru 36 Ya Faɗa Rijiya Ya Mutu a Kano

A wani labarin, wani mutum mai shekaru 36, mai suna Nuhu Rabiu, a ranar Talata ya rasu a Kano jim kadan bayan an ciro shi daga wata rijiya da ya fada ciki, kamar yadda The Punch ta rahoto.

Kara karanta wannan

ICPC ta fallasa dabarar da ‘Yan Majalisa su ke yi, su na yin awon gaba da dukiyar talakawa

Da ya ke tabbatar da afkuwar lamarin, mai magana da yawun hukumar kwana-kwana a Kano, Saminu Yusif Abdullahi, ya ce a sume aka ciro mutumin daga bisani ya rasu.

Ya ce wani Garba Ali ne ya kira su ya sanar da faruwar abin daga nan kuma suka tura jami'ai cikin gaggawa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng