Da duminsa: Jami'an tsaro sun sanya wa gwamnoni 3 ido kan shirin hargitsa Najeriya

Da duminsa: Jami'an tsaro sun sanya wa gwamnoni 3 ido kan shirin hargitsa Najeriya

Gwamnoni uku masu rike da madafun iko a kasar nan sun samu matsala da jami’an tsaro, kan zarginsu da yunkurin tayar da tarzoma da ka iya dabaibaye yankin Arewacin kasar nan, idan aka zuba ido.

Gwamnonin uku, wadanda ke kan wa’adinsu na karshe, rahotanni sun ce an fito da su ne daga shiyyar Arewa maso Gabas da Arewa ta Tsakiya da kuma yankin Kudu-maso-Kudu na siyasar kasar.

Da duminsa: Jami'an tsaro sun sanya wa gwamnoni 3 ido kan shirin hargitsa Najeriya
Da duminsa: Jami'an tsaro sun sanya wa gwamnoni 3 ido kan shirin hargitsa Najeriya. Hoto daga Vanguardngr.com
Asali: UGC

Gwamnonin uku kamar yadda jaridar Vanguard ta samu sun bayyana cewa, sun yi ganawar sirri ne a wani wuri inda suka tsara shirin gudanar da zanga-zanga a fadin kasar, wanda zai dauki salon zanga-zangar ta # ENDSARS na shekarar 2020 tare da durkusar da al'ummar kasar da nufin yin zanga-zanga.

Kara karanta wannan

Ku tara min kudi na gaji Buhari: Dan takara na neman tallafin 'yan soshiyal midiya

Karkashin shirin, daya daga cikin gwamnan arewa maso gabas zai fara shirin gudanar da zanga-zangar gama gari tare da ganawa da manyan masu ruwa da tsaki daga Arewa a Kaduna tare da nuna musu gwamnati ta yi watsi da su kuma yakamata a yi watsi da ita a zaben 2023.

A daya hannun kuma, gwamnonin biyu masu fafutuka a yankin Arewa ta Tsakiya da na Kudu-maso-Kudu za su tunkari gwamnatin tarayya kan yadda ta gaza wajen samar wa ‘yan Nijeriya bukatun yau da kullum ta fuskar samar da man fetur da wutar lantarki da ilimi ga yara tare da bunkasa kabilanci da addini.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Bisa ga dukkan alamu, gwamnan na arewa maso gabas ya gana da wasu kungiyoyi masu ruwa da tsaki kamar kungiyoyin farar hula, shugabannin kwadago, dalibai da kuma ‘yan siyasa da ba su ji dadi ba a Kaduna a farkon makon domin neman amincewarsu kan zanga-zangar da ya shirya.

Kara karanta wannan

Yajin Aikin ASUU: Ƙungiyar Daliban Najeriya Ta Yi Barazanar Fara Zanga-Zanga A Ƙasa

Taron na Kaduna, a cewar hukumar tsaro, ya tattauna dalla-dalla yadda za a hada daliban Najeriya da ke fama da matsalolin da kungiyar malaman jami’o’i, ASUU ta tilasta musu komawa gida, inda za su fuskanci gwamnatin tarayya.

Suna sonkungiyoyi masu zaman kansu, da kuma wasu ‘yan siyasa da suka fusata su shiga cikin kungiyar shirya zanga-zangar gama-gari don yin rijistar irin tasirin da zanga-zangar ENDSARS ta 2020 ta yi a duk faɗin ƙasar.

A cewar makircin da gwamnonin uku ke shirin yi, zanga-zangar da suka shirya yi ita ce ta sa ‘yan Najeriya su ki amincewa da gwamnati mai ci su zabi sabuwar gwamnati saboda zabe mai zuwa ya kusa.

Sai dai wani babban jami’in tsaro da ke sa ido kan ayyukan gwamnonin uku ya shaida wa Sunday Vanguard cewa duk da cewa ba sa adawa da ‘yancin kungiyoyi da zanga-zanga, amma sun damu cewa zanga-zangar da aka shirya za ta iya rikidewa zuwa tashe-tashen hankula na kasa da zai yi wuya a shawo kan lamarin.

Kara karanta wannan

Babu ruwana: Babban sakataren gwamnatin Katsina ya karyata cewar yana da hannu a fashi da makami

“Don haka ne hukumarmu da ‘yan uwanmu na tsaro suka sanya wa gwamnonin nan uku a ido akai-akai kuma za mu sanya ido a kan ayyukansu don ganin ba su jefa al’umma cikin rikicin da za a iya kaucewa ba,” in ji wani babban jami’in gwamnatin tarayya.
“Mun kuma tura mutanenmu zuwa wuraren hasashe don tabbatar da cewa kasar nan ba ta shiga tsaka mai wuya daga miyagun ‘yan siyasa da suka kusan kawo karshen wa’adin mulkinsu kuma ba su damu ba ko kasar ta kone ko a’a,” in ji jami’in a daren jiya. .

Abba Kyari ya sake shiga 3, kwamitin binciken EndSARS na bukatar NDLEA ta mika shi

A wani labari na daban, a kwamitin dake bincikar zargin take hakkin bil'adama da tsohuwar hukumar SARS ta 'yan sandan Najeriya ke yi, ta yi kira ga Hukumar yaki da fasa-kwabrin miyagun kwayoyi da ta mika dakataccen DCP Abba Kyari gaban ta.

Kara karanta wannan

Aiki kai tsaye ga masu 1st Class: Majalisa ta tattauna kan daukar masu digiri aiki

Kwamitin mai zaman kanta ta bukaci shugaban NDLEA, Buba Marwa, da ya mika ma ta Kyari a ranar Talata, 22 ga watan Maris.

Daily Nigerian ta ruwaito yadda, Shugaban kwamitin, Alkali mai ritaya Suleiman Galadima, wanda John Martin ya gabatar, ya umarci kwamandan na IGP-IRT, Tunde Disu, da ya tabbatar an gabatar da Kyari a wannan ranar.

Asali: Legit.ng

Online view pixel