Wani Matashi da ba a San da Zaman Shi ba, Yace Gwamnan Najeriya ne Mahaifinsa

Wani Matashi da ba a San da Zaman Shi ba, Yace Gwamnan Najeriya ne Mahaifinsa

  • An samu wani ‘Dan shekara 27 da ya je kotu, yana cewa Gwamna Babajide Sanwo-Olu shi ne Mahaifinsa
  • John Aikpokpo-Martins shi ne Lauyan da ya tsayawa Emmanuel Sanwo-Olu, yana karar Gwamnan Legas
  • Wannan mutumi yana zargin Gwamnan ya samu alaka da mahaifiyarsa a garin Delta a shekarun 1994/95

Delta - Ana shari’ar nasaba a wata babban kotun jiha mai zama a Effurun a karamar hukumar Uvwie da ke jihar Delta da Gwamna Babajide Sanwo-Olu.

Jaridar Tribune tace wani Emmanuel Sanwo-Olu mai shekara 27 yana ikirarin Gwamnan jihar Legas na mahaifinsa, ya kuma ce ya tabbata da haka.

Emmanuel Sanwo-Olu yake cewa mahaifiyarsa ta sanar da shi cewa Mai girma Babajide Sanwo-Olu ne mahaifinsa, daga baya ta auri wani mutumin.

“Ni dai ina so in ga mahaifina ne, shekaru 27 da suka wuce, ban ga mahaifi na ba.”

Kara karanta wannan

Cin amana: Malamin makaranta ya ba abokinsa gubar bera, ya sace motarsa a Katsina

- Emmanuel Sanwo-Olu

Mahaifi yana daula, yaro yana aikatau

A halin yanzu wannan mutumi mai ‘ya ‘ya uku yace yana yi wa mutane aiki ne domin ciyar da iyalinsa, yayin da mahaifinsa ke gidan gwamnati.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

John Aikpokpo-Martins Esq wanda shi ne Lauyan da ya tsayawa Emmanuel Sanwo-Olu wajen shigar da kara a kotu, yace an fara sauraron shari’arsu.

Gwamnan Najeriya
Gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo Olu Hoto: businessday.ng
Asali: UGC

Ba a shari'a da Gwamnoni

Daily Trust ta rahoto John Aikpokpo-Martins yana cewa Lauyoyin Gwamnan Legas sun bukaci ayi watsi da karar domin doka ta ba gwamnoni kariya.

A cewar Lauyan, ya roki kotu ta ba su dama a kira Gwamna Sanwo-Olu domin ayi masa gwajin DNA, yace ta haka za a san gaskiyar ikirarin da suke yi.

Rahoton ya nuna shi ma Aikpokpo-Martins bai shiryawa shari’ar ba, ya bukaci Alkali ya ba su lokaci domin su zauna da bangaren wadanda ake tuhuma.

Kara karanta wannan

2023: Wasu Karin Jiga-Jigan APC Sun Aje Tafiyar Tinubu, Sun Koma Bayan Wanda Suke Fatan Ya Gaji Buhari

Maganar da ake yi an daga shari’ar mail amba EHC/148/2022 sai zuwa ranar 17 ga Junairun 2023. A nan za a san mataki na gaba da kotu za ta dauka.

Ana zargin Gwamnan mai-ci ya samu alaka da mahaifiyar mai karar, Grace Moses a 1994.

Za a kara FMC a Katsina

Ana kukan babu asibitocin tarayya a Kano, Kaduna, Sokoto, Borno, Akwa-Ibom, Edo, Anambra, Ebonyi da Enugu, sai ga rahoto za a sake gina wani a Katsina.

A kasafin karshe na Mai girma Muhammadu Buhari, gwamnatin tarayya za ta kashe N500m domin samar da katafaren asibitin na biyu a jihar shugaban kasa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel