Iran da Amurka Za Su Sake Zama don Kawo Karshen Yaki
- Tawagogin Amurka da Iran sun kasa cimma yarjejeniya a zaman farko da suka yi domin kawo karshen yakin da ake yi a Gabas ta Tsakiya
- Majiyoyi sun bayyana cewa za a sake zama domin gudanar da zagaye na biyu na tattaunawar a birnin Islamabad na kasar Pakistan
- Tuni dai aka sanar da bangarorin biyu kan bukatar su sake zama domin ci gaba da tattaunawar da aka fara
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Birnin Islamabad, Pakistan - Akwai yiwuwar tawagogin tattaunawa daga Amurka da Iran su koma ƙasar Pakistan a ƙarshen wannan mako.
Tawagogin za su koma ne domin ci gaba da tattaunawa kan kawo ƙarshen yaƙi a yankin Gabas ta Tsakiya.

Source: Getty Images
Tashar Reuters ta ce jami’an Pakistan da na Iran suka bayyana mata hakan a ranar Talata, 14 ga watan Afirilun 2026.
Amurka da Iran za su sake zama
Hakan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan da tattaunawar farko ta ƙare ba tare da an cimma wata matsaya ba.
Har yanzu dai babu wani tabbaci daga jami’an Amurka game da wannan shiri, wanda jami’an Iran da na Pakistan suka tattauna a matsayin sirri ba tare da an bayyana sunayensu ba.
Wata majiya da ke da masaniya kan tattaunawar ta ce an riga an aika wa Washington da Tehran wata shawara na cewa tawagogin su koma Islamabad domin ci gaba da tattaunawa.
Yaushe za a sake zama?
Ko da yake ba a tsayar da takamaiman rana ba, ƙasashen biyu na iya komawa tattaunawar tun a ƙarshen wannan mako.
Wani jami’i a ofishin jakadancin Iran da ke Islamabad ya ce:
“Za a iya gudanar da zagaye na gaba na tattaunawar a ƙarshen wannan mako ko kuma farkon mako mai zuwa. Amma kawo yanzu ba a kammala komai ba.”
Tun da fari, wata babbar majiya daga Iran ta bayyana cewa:
"Ba a sanya takamaiman rana ba, amma tawagogin sun ware ranar Juma’a zuwa Lahadi a matsayin ranakun da za su iya zama.”
Haka zalika, wani babban jami’in Pakistan ya ce Islamabad ta tuntuɓi Iran “kuma mun samu amsa mai kyau cewa a shirye suke su halarci zagaye na biyu na tattaunawar.”

Source: Twitter
Ba a ji ta bakin Amurka da Pakistan ba
Wannan taro na ƙarshen makon da ya gabata shi ne karon farko da jami’an Amurka da na Iran suka fuskanci juna kai-tsaye cikin fiye da shekara 10 kuma shi ne tattaunawa mafi girma tsakanin ƙasashen biyu tun bayan Juyin Juya Halin Musulunci na 1979 a Iran.
Kawo yanzu, ma’aikatar wajen Pakistan, rundunar sojoji, da ofishin firaminista ba su ba da amsa ba kan buƙatar jin ta bakinsu dangane da lamarin.
Fadar White House ma ba ta ba da martani nan take ba.
Donald Trump ya yi barazana ga Iran
A wani labarin kuma, kun ji cewa Shugaban kasar Amurka, Donald Trump, ya sake yin barazana ga Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
Trump ya yi barazanar lalata duk wani jirgin ruwan yakin Iran da ya tunkari shingen da dakarun sojojin Amurka suka kafa kan tashoshin jiragen ruwan kasar.
Barazanarsa na zuwa ne duk da kiraye-kirayen da ƙasashen duniya ke yi na a girmama yarjejeniyar tsagaita wuta tare da komawa teburin tattaunawa.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng


