Da Duminsa: An Yi Wa Tsohon Gwamnan Najeriya Tiyata A Baya, Hotuna Da Bidiyo Sun Fito

Da Duminsa: An Yi Wa Tsohon Gwamnan Najeriya Tiyata A Baya, Hotuna Da Bidiyo Sun Fito

  • An yi wa tsohon gwamna a Najeriya, Ayodele Fayose tiyata a bayansa a wani asibiti a kasar waje
  • An yi masa tiyatan cikin nasara bayan tsohon gwamnan na Jihar Ekiti ya samu rauni a yayin zaben gwamna na jiharsa a 2018
  • Hadimin Fayose a bangaren watsa labarai, Lere Olayinka, ya ce an yi wa mai gidansa tiyata sai biyu cikin watanni shida

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

An yi wa tsohon gwamnan Jihar Ekiti, Ayodele Fayose tiyata a bayansa a wani asibit a kasar waje.

An ga tsohon gwamnan na Jihar Ekiti, wanda ya sha kaye hannun wanda ya gaje shi, Kayode Fayemi, a bidiyo tare da likitoci da malaman jinya suna kula da shi a asibiti.

A cewar dan uwansa, Isaac da kuma tsohon hadiminsa, Lere Olayinka, wannan shine karo na biyu da aka yi wa tsohon gwamnan tiyata a cikin watanni biyar.

Kara karanta wannan

An kai wa 'Dan Majalisar Daura, 'Danuwan Shugaba Buhari Hari Har Gida a Katsina

Ayo Fayose
Bidiyo Da Hotunan Fayose Yayin Da Aka Masa Tiyata a Kasar Waje. Hoto: Lere Olayinka.
Asali: Instagram

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

A faifan bidiyon, an ga Fayose, wanda jigo ne a jam'iyyar Peoples Democratic Party PDP ana taimaka masa ya zauna.

An tattaro cewa tsohon gwamnan na Ekiti ya samu rauni a bayansa a 2018 hakan ya sa aka yi masa tiyatan.

Ga hotuna da bidiyon Fayose a asibitin.

Da ya ke martani kan lamarin, mataimaki na musamman kan bangaren sabuwar kafar watsa labarai na Fayose, Lere Olayinka, ya taya mai gidansa murna bisa yin tiyatar cikin nasara.

Olayinka ya ce:

"Fayose ya yi tiyata sai biyu cikin watanni biyar. Manyan tiyata biyu cikin watanni biyar.
"Guda daya a watan Fabrairu a wutansa yanzu kuma wani guda daya a baya. Sakamakon harin da aka kai masa yayin zaben gwamnan Ekiti a 2018. Wannan ikon Allah ne. Ina maka fatan samun sauki cikin gaggawa Osokomole."

Kara karanta wannan

Kamfanin Dubai Mai Ma’aikata 61,000 Ta Karrama Dan Najeriya A Matsayin Gwarzon Wata

Atiku ya shiga tsaka mai-wuya a 2023, Fayose ya ce har abada Wike ba zai goyi bayansa ba

A wani rahoton, tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Peter Fayose, ya yi bayanin abin da ya sa Nyesom Wike ba zai taba goyon bayan Atiku Abubakar a zaben 2023 ba.

A wata hira da Premium Times ta yi da Ayo Peter Fayose, ya fadi dalilin Gwamna Nyesom Wike na juya baya ga ‘dan takaran na PDP a zaben shugaban kasa.

Fayose ya kara nanata matsayarsa na cewa bayan Muhammadu Buhari ya kammala shekara takwas, abin da ya kamata shi ne shugabanci ya koma kudu.

Asali: Legit.ng

Online view pixel