Insha Allahu bana yan Najeriya zasu yi aikin Hajji, Hukumar jin dadin Alhazai NAHCON

Insha Allahu bana yan Najeriya zasu yi aikin Hajji, Hukumar jin dadin Alhazai NAHCON

  • Kwamishana a hukumar NAHCON ya bayyana cewa da yardar Allah za'a tafi Hajji bana
  • Gwamnatin kasar Saudiyya ta sassauta dokokin kariya daga COVID-19 a Makkah da Madina
  • Kowace shekara kimanin yan Najeriya 90,000 ke zuwa aikin Hajji

Hukumar jin dadin alhazan Najeriya NAHCON ta bayyana cewa da yardar Ubangiji bana maniyyata a Najeriya zasu samu zuwa kasa mai tsarki don gudanar da aikin Hajji

Wannan ya biyo bayan soke dokokin kariya daga cutar COVID-19 da gwamnatin kasar Saudiyya tayi a farkon makon nan.

Kwamishanan hukumar mai wakiltar al'ummar yankin kudu maso kudu, Musa Sadiq Oniyesaneyene, a hirarsa da Legit Hausa ya bayyana cewa ko makonnin baya ya shiga Saudiyya kuma da yardar Allah bana za'a tafi.

A cewarsa:

Kara karanta wannan

Muna farin cikin soke dokokin COVID-19 a Masallacin Makkah da Madina: Hukumar jin dadin Alhazai

"Dubi ga yadda abubuwa ke gudana yanzu, Insha Allahu ya kamata ayi kuma za'a yi.
'"Saboda sassauta dokokin kariya daga cutar Korona a Saudiya da kuma maganar cewa an cire dokar kayyade maniyyata masu shiga Harami, tabbas za'a yi Hajji."
"Ko watanni biyu da suka gabata na tafi Saudiyya wasu ayyuka, mun fuskanci matsaloli, ni kaina na fuskanci wadannan matsaloli amma sai da aka tilasta ni zama a Madina cikin dakin Otal da, hakazalika a Makkah."
"Amma muna kyautata zaton cewa yanzu an cire wadannan dokoki."

Insha Allahu bana yan Najeriya zasu yi aiki Hajji, Hukumar jin dadin Alhazai NAHCON
Insha Allahu bana yan Najeriya zasu yi aiki Hajji, Hukumar jin dadin Alhazai NAHCON Hoto: Sadiq Musa
Asali: Facebook

An daina bada tazara a sahun Sallah daga Lahadi a Makkah da Madina

Mun kawo muku cewa Hukumomi a Masallatai biyu mafi daraja a duniya sun yi watsi da dokar wajabta baiwa juna tazara yayin Sallah a Masallacin Haram dake Makkah da Masjid Al Nabawi dake Madina.

Kara karanta wannan

Bidiyon limamin Makkah na kira a daidaita sahu, karon farko sama da shekara guda

An yi watsi da wannan doka ne fari daga ranar Lahadi, 17 ga watan Oktoba, 2021.

Sheikh AbdulRahman Sudais ne shugaban Masallatan Biyu.

Wata majiya a fadar Sudais ta bayyana cewa za'a cire dokar bada tazaran ne daga ranar Asabar bayan Sallar Isha, rahoton Haramain Sharifain.

Asali: Legit.ng

Online view pixel