Muhammad Malumfashi
20340 articles published since 15 Yun 2016
20340 articles published since 15 Yun 2016
Gwamnatin Najeriya ta kaddamar da shirin samar da ayyukan yi a fadin dukkan jihohi. Karamar ministar kwadago, Nkeiruka Onyejeochace ta bayyana haka a Legas.
Peter Obi ya tabbatar da cewa zai sake tsayawa takarar shugaban kasa a 2027, yana mai cewa zai canza Najeriya cikin shekaru hudu idan aka zabe shi.
Fayose ya ce Obi ne kadai mai tasiri a ƴan adawa, kuma ADC ba za ta kai labari a 2027 ba, yayin da ya fadi dalilin ƙin karbar tayin mukami da Tinubu ya yi masa.
Taron malaman Arewa da aka yi a Kaduna ya tattauna matsalar rashin tsaro da habaka tattalin arziki. Sarkin Musulmi ya bukaci a hada kai a Arewa domin cigaba.
A labarin nan, za a ji cewa tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar ya bayyana cewa Ministan Tinubu ya fadi gaskiya kan kwangilar titin Legas zuwa Calabar.
Dan majalisar jihar Jigawa mai wakiltar karamar hukumar Duste, Hon. Tasiu Ishaq Soja ya raba kayan tallafin da kudinsu ya kai N250m. Gwamna Umar Namadi ya yaba masa
Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayodele Fayose, ya yi magana kan rikicin jam'iyyar adawa ta PDP. Fayose ya bayyana cewa wasu gwamnoni za su yi murabus daga jam'iyyar.
Ministan yada labarai da wayar da kan jama'a, Mohammed Idris, ya bayyana cewa gwamnonin jam'iyyun adawa da dama na son shigowa jam'iyyar APC mai mulki.
NBS ta ce hauhawar farashin kaya a Najeriya ta ragu zuwa 18.02% a Satumba 2025 — mafi ƙanƙanta cikin shekaru uku, yayin da farashin abinci ya fadi zuwa 16.87%.
Muhammad Malumfashi
Samu kari