Biden: Ba mu da matsala da Taliban wajen debe 'yan uwanmu Amurkawa a Afghanistan

Biden: Ba mu da matsala da Taliban wajen debe 'yan uwanmu Amurkawa a Afghanistan

  • Joe Biden na Amurka ya bayyana cewa, Amurka ba ta fuskantar kalubalen kwashe mutanenta a Afghanistan
  • A cewarsa, matsalar ita ce debe mutanen da suke goya wa Amurka baya a kasar wadanda ba sa son zama da Taliban
  • Shugaban ya ce Amurka za ta ci gaba da zama a kasar har sai ta kwashe dukkan Amurkawa a kasar

Afghanistan - Shugaba Joe Biden na kasar Amurka ya ce Taliban na ba da hadin kai ga Amurka dangane da kwashe Amurkawa a Afghanistan, Daily Trust ta tattaro.

Tun bayan rugujewar gwamnati a Afganistan a makon da ya gabata, sojojin Amurka suna kwashe 'yan Amurka daga kasar.

A cikin hirar sa ta farko tun bayan da Taliban ta karbe iko a Afghanistan, Biden ya fadawa ABC News cewa duk da hadin kan da ake bayarwa wajen fitar da Amurkawa daga kasar, “muna kara samun matsala” wajen kwashe ‘yan Afghanistan da ke hada kai da Amurka.

Biden: Ba mu da matsala da Taliban wajen debe 'yan uwanmu Amurkawa a Afghanistan
Shugaban Amurka Joe Biden | Hoto: aljazeera.com
Asali: UGC

Ya ce:

"Suna ba da hadin kai, suna barin 'yan Amurka su fita, ma'aikatan Amurka su fita, ofisoshin jakadanci su fita, da dai sauransu, amma muna samun karin wahalar samun wadanda suka taimaka mana lokacin da muke can."

Ya kuma ce sojoji ba za su bar wani Ba'amurke a Afghanistan ba, koda kuwa hakan na nufin zama cikin Kabul na tsawon shekaru fiye da yadda aka amince.

Biden ya kara da cewa:

"Idan akwai sauran jama'ar Amurka da suka rage, za mu zauna har sai mun fita da su duka."

Jaridar New York Times ta ce, da aka tambaye shi ko yana tunanin magance rikicin zai iya tafiya?

Biden ya ce:

"A'a. Za mu koma hangen nesa mu duba, amma ra'ayin cewa ko ta yaya, akwai wata hanyar da za mu fita ba tare da hargitsi ba, ban san yadda hakan ke faruwa ba."

'Yan majalisar dokokin Amurka sun matsa a kara wa'adin kwashe Amurkawa a Afghanistan

'Yan majalisar dokokin Amurka sun matsa wa Biden ya tsawaita wa'adin kwashewar zuwa ranar 31 ga watan Agusta da ya tsara don ficewa gaba daya.

Amurka ta ce ta kwashe kusan mutane 6,000 daga Afghanistan tun ranar Asabar amma dubunnan Amurkawa da dubun dubatan 'yan Afghanistan da ke son barin kasar na ci gaba da kasancewa kuma tana da jinkirin debewar lamarin da ke jefa rayuwa cikin hadari.

'Yan mata masu ilimi, tsoffin masu fassara ga sojojin Amurka da sauran 'yan Afghanistan da ke cikin hadarin gaske daga Taliban sun yi kira ga gwamnatin Biden da ta gaggauta gwaso su zuwa Amurka.

Shugaban Afghanistan ya tsere da makudan kudade cike da jirgi da motoci

A wani labarin, Ofishin jakadancin Rasha da ke Kabul ya fada a ranar Litinin 16 ga watan Agusta cewa, shugaban Afghanistan Ashraf Ghani ya tsere daga kasar da motoci hudu da jirgi mai saukar ungulu cike da tsabar kudi har suna zuba.

Ghani, an ce ya bar Afghanistan ranar Lahadi yayin da Taliban ta shiga Kabul, wanda a cewarsa yana son kaucewa zubar da jini, a cewar Independent.

Kamfanin dillancin labaran RIA ya nakalto Nikita Ishchenko, mai magana da yawun ofishin jakadancin Rasha a Kabul yana cewa:

"Dangane da rugujewar tsarin mulki (mai barin gado), ya shahara da yadda Ghani ya tsere daga Afghanistan."

Asali: Legit.ng

Online view pixel