Da dumi-dumi: Mutane da dama sun jikkata yayinda abun fashewa ya tashi a kasuwar Port Harcourt

Da dumi-dumi: Mutane da dama sun jikkata yayinda abun fashewa ya tashi a kasuwar Port Harcourt

- Wani abun fashewa ya tashi a wasu sassa na kasuwar mile 3 a karamar hukumar Port Harcourt, jihar Ribas

- Mutane da dama sun jikkata yayinda lamarin ya haifar da tsoro a tsakanin al’umman yankin

- Rundunar yan sanda a jihar ta ce jami’anta na hanyar zuwa wajen don tabbatar da lamarin

Wani abun fashewa ya tashi a wasu sassa na kasuwar mile 3 a karamar hukumar Port Harcourt, jihar Ribas jaridar The Nation da Vanguard suka ruwaito.

Lamarin, wanda ya faru da misalin karfe 6:30 na safiyar ranar Litinin, 31 ga watan Mayu, ya sanya mutane musamman a tashar motoci ta Mile 3 gudu zuwa wurare daban-daban don tsiratar da rayuwarsu.

KU KARANTA KUMA: Matasan Zamfara sun toshe babbar hanya, sun lalata ababen hawa a wata mummunar zanga-zanga da suke gudanarwa

Da dumi-dumi: Mutane da dama sun jikkata yayinda abun fashewa ya tashi a kasuwar Port Harcourt
Da dumi-dumi: Mutane da dama sun jikkata yayinda abun fashewa ya tashi a kasuwar Port Harcourt
Source: Original

Kodayake ba a rasa rai ba, amma rahotanni sun ce mutane da yawa sun ji rauni.

Wata majiya a cikin kasuwar ta ce fashewan abun ya haifar da tsoro a yankin.

Kakakin rundunar 'yan sanda na Ribas, SP. Nnamdi Omoni, ya ce ‘yan sanda na kan hanyarsu ta zuwa yankin don tabbatar da faruwar lamarin.

KU KARANTA KUMA: 'Yan bindiga sun nemi a biya kudin fansa naira Miliyan 50 domin sakin wadanda aka sace a Neja

A wani labarin, mun ji cewa Ƴan bindiga sun halaka kimanin mutane 12 a harin da suka kai a wasu garuruwa a ƙaramar hukumar Ako a jihar Benue, Daily Trust ta ruwaito.

Shaidun gani da ido sun ce an kai hare-haren ne a lokuta guda daga daren ranar Asabar da Safiyar Lahadi a Tologa, Ndi-Obasi, Odoken duk a mazabar Ekile a ƙaramar hukumar Ado.

Shugaban karamar hukumar Ado, James Oche, ya shaidawa manema labarai a Makurdi a wayan tarho cewa an kashe mutane 12 yayin hare-haren da aka kai a ƙauyuka biyar a garin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng