Da dumi-dumi: Mutane da dama sun jikkata yayinda abun fashewa ya tashi a kasuwar Port Harcourt
- Wani abun fashewa ya tashi a wasu sassa na kasuwar mile 3 a karamar hukumar Port Harcourt, jihar Ribas
- Mutane da dama sun jikkata yayinda lamarin ya haifar da tsoro a tsakanin al’umman yankin
- Rundunar yan sanda a jihar ta ce jami’anta na hanyar zuwa wajen don tabbatar da lamarin
Wani abun fashewa ya tashi a wasu sassa na kasuwar mile 3 a karamar hukumar Port Harcourt, jihar Ribas jaridar The Nation da Vanguard suka ruwaito.
Lamarin, wanda ya faru da misalin karfe 6:30 na safiyar ranar Litinin, 31 ga watan Mayu, ya sanya mutane musamman a tashar motoci ta Mile 3 gudu zuwa wurare daban-daban don tsiratar da rayuwarsu.
KU KARANTA KUMA: Matasan Zamfara sun toshe babbar hanya, sun lalata ababen hawa a wata mummunar zanga-zanga da suke gudanarwa
Kodayake ba a rasa rai ba, amma rahotanni sun ce mutane da yawa sun ji rauni.
Wata majiya a cikin kasuwar ta ce fashewan abun ya haifar da tsoro a yankin.
Kakakin rundunar 'yan sanda na Ribas, SP. Nnamdi Omoni, ya ce ‘yan sanda na kan hanyarsu ta zuwa yankin don tabbatar da faruwar lamarin.
KU KARANTA KUMA: 'Yan bindiga sun nemi a biya kudin fansa naira Miliyan 50 domin sakin wadanda aka sace a Neja
A wani labarin, mun ji cewa Ƴan bindiga sun halaka kimanin mutane 12 a harin da suka kai a wasu garuruwa a ƙaramar hukumar Ako a jihar Benue, Daily Trust ta ruwaito.
Shaidun gani da ido sun ce an kai hare-haren ne a lokuta guda daga daren ranar Asabar da Safiyar Lahadi a Tologa, Ndi-Obasi, Odoken duk a mazabar Ekile a ƙaramar hukumar Ado.
Shugaban karamar hukumar Ado, James Oche, ya shaidawa manema labarai a Makurdi a wayan tarho cewa an kashe mutane 12 yayin hare-haren da aka kai a ƙauyuka biyar a garin.
Asali: Legit.ng