El-Rufai Yana Nema Wa Hukumomin Tsaro Kudi, Ya Koka Kan Karuwar Fashi da Makami

El-Rufai Yana Nema Wa Hukumomin Tsaro Kudi, Ya Koka Kan Karuwar Fashi da Makami

- Gwamna Nasir El-Rufai na jihar Kaduna ya koka a kan karuwar satar mutane da fashi da makami a jihar da sauran sassan kasar

- El-Rufai na nema wa hukumomin tsaro kudade domin karfafa yaki da ta'addanci

- Ya yi Alla-wadai tare da kira ga dukkan 'yan kasa da su yi hakuri da kuma mara wa jami'an tsaro baya don magance matsalar

Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya nuna damuwar sa dangane da karuwar satar mutane da fashi da makami a jihar da sauran sassan kasar.

Gwamnan ya bayyana cewa lamarin na karuwa a kullum kuma yana daukar matakin ban tsoro, don haka yake neman kudade ga hukumomin tsaro Channels TV ta ruwaito.

KU KARANTA KUMA: Boko Haram: Ndume Ya Tona Daga Inda Yan Ta’adda Ke Samun Makamai da Alburusai

El-Rufai Yana Nema Wa Hukumomin Tsaro Kudi, Ya Koka Kan Karuwar Fashi da Makami
El-Rufai Yana Nema Wa Hukumomin Tsaro Kudi, Ya Koka Kan Karuwar Fashi da Makami Hoto: @elrufai
Asali: Facebook

Gwamna El-Rufai ya bayyana hakan ne a ranar Juma'a yayin gabatar da rahoton farko na Tsaro da Ma'aikatar Tsaro da Harkokin Cikin Gida ta jihar ta gabatar.

Ya bayyana halin da 'yan kasa ke ciki a yanzu haka a jihar ta Kaduna da ma kasa baki daya a matsayin abin takaici da kuma ci gaba da rasa yarda da jami'an tsaro saboda hare-haren.

A cewarsa, 'yan ta'addan da ke gudanar da ayyukansu a cikin jihar ta Kaduna suna kara kusantowa daga kauyukan karkara zuwa biranen, inda suke kai hare-hare tare da kashe' yan kasa ba tare da tsoro ba.

Ya kuma yi kira ga dukkan 'yan kasa da su yi hakuri tare da mara wa jami'an tsaro baya don magance matsalar, duk da cewa ya na kuma bukatar samar da isassun kudade ga hukumomin tsaro don ba su damar yin aiki mai kyau.

KU KARANTA KUMA: APC Za Ta Kai Ƙarar Mbaka Wurin Fafaroma Saboda Yi Wa Buhari Barazana

Da yake gabatar da rahoton tsaron, kwamishinan tsaro na cikin gida da harkokin cikin gida na Kaduna, Samuel Aruwan ya bayyana cewa jimillar mutane 323 aka kashe daga watan Janairu zuwa Maris 2021, daga cikinsu 292 maza ne kuma mata 20.

Aruwan ya kuma ce, kimanin mutane 948 ne 'yan ta'adda suka yi garkuwa da su a tsakanin lokacin da ake dubawa yayin da shiyyar Kaduna ta tsakiya ita kadai ta samu mutane 236 da aka kashe a cikin kananan hukumomin Birnin Gwari, Chikun, Igabi, da Kajuru.

A wani labarin, shugaban kasa Muhammadu Buhari yana nan yana jagorantar taron majalisar tsaro a fadar Shugaban kasa da ke babbar birnin tarayya, Abuja.

Daga cikin wadanda suka halarci taron akwai mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo, Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha.

Sai Shugaban Ma'aikatan Fadar shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari, NSA Manja Janar Babagana Monguno (mai murabus) da kuma wasu ministoci.

Asali: Legit.ng

Online view pixel