Saura Kiris allurar Covid 19 ta iso Nigeria, Boss Mustapha

Saura Kiris allurar Covid 19 ta iso Nigeria, Boss Mustapha

- Kwamitin shugaban kasa kan Covid-19 sun sanar da cewa farkon watan Fabrairu rigakafin Korona zai shigo Najeriya

- Sakataren kwamitin ya bayyana cewa har yanzu kwayar cutar hau-hawa take yi a Najeriya

- Ya kuma bukaci 'yan Najeriya da su bada hadin kai wajen yaki da cutar ta Korona

Jirgin farko na allurar rigakafi 100,000 na Covid-19 mallakar Najeriya, zai iso farkon watan Fabrairu, PM News ta ruwaito.

Mista Boss Mustapha, sakataren Gwamnatin Tarayya kuma shugaban kwamitin fadar Shugaban kasa kan COVID-19, ne ya sanar da hakan yau a Abuja.

A cewarsa, kokarin samun dama da tura alluran rigakafi na ci gaba kuma kamar yadda COVAX ta riga ta sanar, 100,000 na farko da Najeriya ke tsammani yanzu zai isa a farkon makonnin Fabrairu.

KU KARANTA: 'Yan sandan Najeriya sun fi na kowace kasa kwarewa a duniya - IGP

Allurar rigakafin COVID-19 na kiris da isowa Najeriya - Boss Mustapha
Allurar rigakafin COVID-19 na kiris da isowa Najeriya - Boss Mustapha Hoto: Federal Ministry of Information and Culture
Asali: UGC

“Muna so mu tabbatar wa da 'yan Nijeriya cewa alluran rigakafin za su kasance cikin aminci da tasiri idan aka kawo su. Muna kira ga kowa da kowa da a shiga cikin yaki don kawar da jinkirin yin rigakafin.

Kwamitin ya kuma bayyana yadda cutar take kara yaduwa a Najeriya.

Ya zuwa ranar 24 ga Janairu, Nijeriya na da mutane 121,566 da aka tabbatar da sun kamu; jimlar gwaje-gwaje a yanzu sun kai 1,270,523, yayin da masu jinya suka kai 22,834.

KU KARANTA: 'Yan bautar kasa 13 sun kamu da COVID-19 a sansanin NYSC

A wani alabarin, Likitocin lafiya uku sun mutu yayin da wasu 53 suka kamu da kwayar ta COVID-19 tun bayan bullar kwayar cutar a jihar Kano, in ji Dakta Usman Ali, shugaban kungiyar likitocin Nijeriya (NMA), Daily Trust ta ruwaito.

Usman a wata hira da ya yi da manema labarai ya ce mutuwar ta kwanan nan ta wani kwararrun masanan cututtukan da suka mutu a wata cibiyar keɓewa a ranar Litinin a makon da ya gabata.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel