Saura Kiris allurar Covid 19 ta iso Nigeria, Boss Mustapha

Saura Kiris allurar Covid 19 ta iso Nigeria, Boss Mustapha

- Kwamitin shugaban kasa kan Covid-19 sun sanar da cewa farkon watan Fabrairu rigakafin Korona zai shigo Najeriya

- Sakataren kwamitin ya bayyana cewa har yanzu kwayar cutar hau-hawa take yi a Najeriya

- Ya kuma bukaci 'yan Najeriya da su bada hadin kai wajen yaki da cutar ta Korona

Jirgin farko na allurar rigakafi 100,000 na Covid-19 mallakar Najeriya, zai iso farkon watan Fabrairu, PM News ta ruwaito.

Mista Boss Mustapha, sakataren Gwamnatin Tarayya kuma shugaban kwamitin fadar Shugaban kasa kan COVID-19, ne ya sanar da hakan yau a Abuja.

A cewarsa, kokarin samun dama da tura alluran rigakafi na ci gaba kuma kamar yadda COVAX ta riga ta sanar, 100,000 na farko da Najeriya ke tsammani yanzu zai isa a farkon makonnin Fabrairu.

KU KARANTA: 'Yan sandan Najeriya sun fi na kowace kasa kwarewa a duniya - IGP

Allurar rigakafin COVID-19 na kiris da isowa Najeriya - Boss Mustapha
Allurar rigakafin COVID-19 na kiris da isowa Najeriya - Boss Mustapha Hoto: Federal Ministry of Information and Culture
Source: UGC

“Muna so mu tabbatar wa da 'yan Nijeriya cewa alluran rigakafin za su kasance cikin aminci da tasiri idan aka kawo su. Muna kira ga kowa da kowa da a shiga cikin yaki don kawar da jinkirin yin rigakafin.

Kwamitin ya kuma bayyana yadda cutar take kara yaduwa a Najeriya.

Ya zuwa ranar 24 ga Janairu, Nijeriya na da mutane 121,566 da aka tabbatar da sun kamu; jimlar gwaje-gwaje a yanzu sun kai 1,270,523, yayin da masu jinya suka kai 22,834.

KU KARANTA: 'Yan bautar kasa 13 sun kamu da COVID-19 a sansanin NYSC

A wani alabarin, Likitocin lafiya uku sun mutu yayin da wasu 53 suka kamu da kwayar ta COVID-19 tun bayan bullar kwayar cutar a jihar Kano, in ji Dakta Usman Ali, shugaban kungiyar likitocin Nijeriya (NMA), Daily Trust ta ruwaito.

Usman a wata hira da ya yi da manema labarai ya ce mutuwar ta kwanan nan ta wani kwararrun masanan cututtukan da suka mutu a wata cibiyar keɓewa a ranar Litinin a makon da ya gabata.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and leads the Hausa Desk at Legit.ng. He is AfricaCheck's ambassador and HumAngle Technology and Civic Impact Fellow. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. His commitment to excellence has earned him recognition, including the Legit Fearless Team Player of the Year 2023 and 2024 Distinguished Editorial Leadership Award. Email: salisu.ibrahim@corp.legit.ng