Siyasar Najeriya
Majalisar dokokin jihar Zamfara ta zaɓi Bilyaminu Moriki a matsayin saɓon kakakinta. Hon. Bilyaminu ya samu hawa kan kujerar shugabancin ba tare da hamayya ba.
Moses Sule, sabon mamba a majalisar dokokin jihar Filato ya yi nasarar zama shugaban majalisa ta 10 yayin bikin rantsuwar kama aiki ranar Talata, 13 ga wata.
Sanata Barau Jibrin ya zama mataimakin shugaban majalisar dattawa a zaɓen da aka gudanar ranar 13 ga watan Yuni. Gogaggen ɗan siyasan ya fito daga jihar Kano.
A ranar Talata, 13 ga watan Yuni ne majalisar dokokin jihar Borno ta sake zabar Hon Abdu;lkarim Lawan a matsayin kakakin majalisa ta 10 karo na hudu a jere.
Sanata Godswill Akpabio, sabon shugaban majalisar dattawa ya ziyarci shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, a fadarsa da ke Abuja bayan lashe zabe ranar Talata.
Bayan sanar da sakamakon wanda ya lashe zabe, a halin yanzu an rantsar da Sanata Godswill Akoabio a matsayin sabon shugaban majalisar dattawa ta 10 daga yau.
Mun tattaro maku tarihin rayuwa da siyasar Sanata Godswill Akpabio da na Sanata Barau Jibrin da su ka gaji Ahmad Lawan da Ovie Omo-Agege a majalisar dattawa
Rahotanni daga majalisar dattawa Najeriya sun nuna cewa fafatawa ta ɗauki zafi tsakanin manyan yan takara guda biyu, Sanata Akpbio da kuma Abdul'aziz Yari.
Kwamitin shari'a ya fito ya kare tsohon gwamnan jihar Kaduna El-Rufai daga sukar da Kungiyar Kiristocin Najeriya, CAN, ta masa game da tikitin muslmi-muslim.
Siyasar Najeriya
Samu kari