Hukumar yan sandan NAjeriya
Rahotanni sun tabbatar da ƴan sanda a jihar Katsina sun halaka miyagun ƴan ta'adda mutum biyu. Ƴan sandan sun kuma kwato muggan makamai a hannun ƴan ta'addan.
Wani matashi ya shiga hannu bayan da ya kwace wayar wata mata da kuma kokarin soka mata wuka a jihar Kano da ke Arewa maso Yamma. Ya bayyanayadda ya yi satar.
Kisihi ya sanya wani matashi aikin dana sani yayin da aka daure shi shekaru bakwai a gidan yari saboda ya watsawa budurwarsa da daurayinta ruwan acid a Legas.
Rahotanni sun tabbatar da aukuwar wani mummunan haɗarin mota wanda ya yi sanadiyyar rasuwar wasu jami'an ƴan sanda mutum uku a ƙaramar hukumar Giwa ta Kaduna.
Rundunar yan sanda reshen jihar Filato sun bayyana cewa sun sami labarin wasu furbatattu na kulla tuggun kai hari zauren majalisar dokokin jiha, ta gargade su.
Tsagerun yan bindiga sun sace kwamishinar hukumar kidaya ta ƙasa mai kula da jihar Bayelsa, Gloria Izonfuo, a kan hanyarta ta zuwa Patakwal, birnin jihar Ribas.
Wasu matasa a jihar Benue sun binne wani tsoho da ransa bisa zargin ya hallaka ahalinsa ta hanyar tsafi da kuma aikata maita da ta kai ga mutuwar ahalin nasa.
Labarin da ke iso mu ya bayyana cewa, wani gini ya ruguje a wani yankin jihar Oyo inda ya hallaka mutanen da ba a san adadinsu ya zuwa yanzu da ake hada rahoto.
Wani ya sari wata budurwa da suke soyayya a hannuwa da fuska, ya yi sanadiyyar ajalinta. Kakakin ‘yan sandan Kaduna, Muhammad Jalige ya nuna bakin kishi ya jawo
Hukumar yan sandan NAjeriya
Samu kari