Hajjin Bana
Hukumar jin daɗin alhazai ta jihar Kebbi ta tabbatar da rasuwar Hajiya Maryamu daga ƙaramar hukumar Maiyama, ta rasu ne a asibitin Sarki Abdul'aziz da ke Makkah.
Rahotanni sun tabbatar da rasuwar wata Hajiya 'yar jihar Neja a kasa mai tsarki yayin gudanar da aikin Hajjin bana na shekarar 2024. Ta rasu ne a birnin Makkah.
Wasu Alhazai mutum biyu na jihar Kebbi sun riga mu gidan gaskiya. Gwamnatin jihar ta tabbatar da rasuwarsu inda ta mika sakon ta'aziyya bisa wannan rashi.
Hukumar NAHCON ta jinjinawa mahajjaci mai suna Muhammad Na'Allah daga yankin Gummi a jihar Zamfara da ya mayar da kudin tsintuwa da suka kai €1,750.
Gwamnan jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya bukaci majalisar tarayya da ta binciki tallafin N90bn da gwamnatin tarayya ta ba hukumar NAHCON domin hajjin bana.
Kungiyar 'yan jarida ta IHR ta jinjinawa hukumar jin dadin alhazai a jihar Kaduna bayan dawowa mahajjata kudi kimanin $50 saboda sauki da aka samu kan hadaya.
Jirgin farko da ya kwaso alhazan Najeriya daga Saudiya ya Iso gida. Kashi na farko na alhazai 410 daga jihar Kebbi da suka yi aikin Hajjin bana sun dawo gida.
Rahotanni sun bayyana cewa Ƙasar Masar ta rasa alhazai 600 waɗanda suka rasu sakamakon tsananin zafin da aka yi fama da shi a aikin hajjin bana a Saudiyya.
Alhaji daga jihar Jigawa ya ƙara ɗaga kimar Najeriya yayin da ya mayar da jakar kuɗin da ya tsinta a Masallacin Annabi SAW a Madinah, ya yi cigiya bai ga mai ita ba.
Hajjin Bana
Samu kari