Zaben Shugaban kasan Najeriya
Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya bayyana cewa idan har yana numfashi a duniya ba zai taɓa jingine siyasa ba a Najeriya.
Hankalin jam’iyyar mai mulki ta APC ta fara karkata kan tattaunawar hadakar Atiku Abubakar na jam'iyyar PDP da takwaransa na LP, Peter Obi gabanin zaben 2027.
Shugaban kungiyar kwadago ta kasa (NLC) Joe Ajaero ya ce ba su da masaniyar tattaunawa tsakanin jam’iyyar LP da wasu ‘yan siyasa a kasar gabanin zaben 2027 ba.
Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya nuna alamun bai hakura da neman mulkin Najeriya ba, ya ce wuƙa da nama na hannun mambobin PDP.
Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa tattaunawarsa da Peter Obi na na duba yiwuwar hadewa wuri guda kafin zabe nag aba, kuma zai marawa wanda ya dace baya.
Kungiyar Kabilar Ibo ta Ohanaeze ta gargadi tsohon dan takarar shugaban kasa a zaben da ya gabata karkashin ya yi hankali da 'yan Arewa a zaben 2027.
Tsohon gwamnan jihar Katsina, Aminu Masari ya ce wadanda ke nadamar zaben Tinubu a 2023 suna hankoro ne saboda ba su samu abinda suke so ba a gwamnatin.
Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya ce ya yi farin cikin karɓar bakuncin tsohon gwamnan Anambra, Peter Obi na jam'iyyar Labour Party.
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ba zai ji dadin kalaman Kashim Shettima ba. Na biyu a Najeriyan ya maida martani ga 'dan takaran PDP a zaben 2023.
Zaben Shugaban kasan Najeriya
Samu kari