Jihar Ekiti
Wasu 'yan mata a sansanin NYSC dake Emure a jihar Ekiti sun tsallake rijiya da baya. Bangon bandaki ya rufta musu yayin da suke shirin yin wanka ranar Juma'a.
Jihohi biyu na Kudu maso Yamma za su fuskanci daukewar wutar lantarki yayin da kamfanin rarraba wutar lantarkin Najeriya ya bayyana shirin gudanar da muhimmin gyara.
Babban Sifetan ƴan sanda, Kayode Egbetokun ya nuna alhini kan rasuwar tsohon kwamishinan ƴan sanda kuma basarake, Oba Emmanuel Adebayo a jihar Ekiti.
Wata kotu a jihar Ekiti ta bada umurnin rataye wasu masu kwacen waya su biyu. An kama mutane dauke da makamai da wayoyi da kudi da suka sace a wajen wasu mutane.
Wani malamin addinin musulunci ya bankawa gidan matarsa wuta a jihar Ekiti saboda ta ki yarda su yi Sallar dare. Jami'an 'yan sanda sun kama shi.
Hukumar jami'ar ilimi, kimiyya da fasaha ta jihar Ekiti ta kori ɗalibai.mata biyu bisa laifin dukan da aka yi wa wata ɗaliba a wani faifan bidiyo da ya bazu a X.
Shugaban karamar hukumar Ikere-Ekiti, Olu Adamolekun ya rantsar da hadimansa da Alkur'ani da kuma gunki inda ya bukace su da su yi biyayya ga jam'iyyar APC.
Babbar kotun jihar Ekiti ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga wasu 'yan fashi da makami guda uku. Kotun ta ce an yanke musu hukunci ne bayan kama su da laifi.
Al'ummar Musulmi a jihar Ekiti sun yabawa Aliko Dangote kan ba su tallafi a dukkan kananan hukumomi inda suka ce tallafin ya zo a dai-dai lokacin da ake bukata.
Jihar Ekiti
Samu kari