Atiku Abubakar
Bayan hukuncin kotun koli na ranar Alhamis, 26 ga watan Oktoba, Ganduje ya bukaci Atiku Abubakar da Peter Obi da su yi takarar shugaban kasa a babban zaben 2031.
An kawo jerin manyan Jam'iyyar PDP da su ka yi wa Tinubu barkan nasara a kotun koli. Irinsu Reno Omokri sun yi farin ciki ne saboda an doke Peter Obi a kotu.
Alkalin Alkalai, Olukayode Ariwoola, ya amince a haska shari'ar kotun kolin Najeriya kan kallubalantar zaben Shugaba Tinubu da jam'iyyun adawa ke kallubalanta.
Shugaban jam'iyyar APC, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya ta ya Tinubu murnar samun nasara a kotun koli, ya shawarci Atiku da Obi su gwada a shekakar 2031.
Sanata Barau I. Jibrin, mataimakin shugaban majalisar dattawa ya yi murna da hukuncin Kotun ƙoli, ya bukaci masu kara su maida wuƙarsu, su zo a haɗa kai a gina ƙasa.
Yayin da ake ci gaba da shari'ar zaben shugaban kasa, kotun koli ta yi watsi da sabbin korafe-korafe da Atiku ke son shigarwa a gabanta, ta ce zai bata mu su lokaci.
Ministan sufurin jiragen sama kuma jigo a jam'iyyar APC, Festus Keyamo, ya buƙaci Atiku Abubakar da Peter Obi su kira Shugaba Tinubu su taya shi murna.
Mai sharhi kan harkokin jama’a, Reno Omokri ya bayyana cewa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi ba zai taba zama shugaban kasar Najeriya ba.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya bayyana jin dadinsa kan nasarar da ya samu a kotun koli da ta yanke hukunci a yau Alhamis 26 ga watan Oktoba.
Atiku Abubakar
Samu kari