Arewa
Rundunar 'yan sanda a jihar Kano sun haramta hawan angonci da kilisa da kuma taron majalisi don dakile matsalar tsaro da ake samu a birnin Kano baki daya.
Jam'iyyar PDP mai adawa a jihar Kebbi ta zargi gwamnan jihar, Kwamred Nasir Idris kan salwantar da makudan kudade har Naira biliyan 20 cikin kwanaki dari kacal.
Gwamnatin Adamawa ta kare kanta dangane da matakin sanya hoton gwamna Ahmadu Finfiri a jikin buhunan shinkafar tallafin rage zafin cire tallafin man fetur.
Allah ya yi wa shahararren malamin addinin Musulunci, Sheikh Giro Argungu rasuwa a yau Laraba 6 ga watan Satumba bayan fama da gajeriyar jinya a Birnin Kebbi.
Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya amince a tura wa kungiyar kwadago NLC reshen jihar Niger manyan Tireloli na Buhunan Shinkafa a matsayin tallafin rage radaɗi.
Kungiyar Kwadago ta Najeriya, NLC reshen jihar Neja ta ki amincewa da tsarin Gwamna Umar Bago na ware ma'aikata a cikin tsarin rabon kayan tallafi a jihar.
Bidiyon wata akuya da ta haifi ɗa mai kama da halittar jikin ɗan Adam a jihar Kwara ya ɗauki hankulan jama'a. An yaɗa bidiyon sosai a kafafen sada zumunta inda.
Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani ya bayyana akdand aga abin da ya gani na hujjojin da jam'iyyar PDP ta bayyana a gaban kotu a kansa da kuma zaben da aka gudanar.
Rahoto ya bayyana yadda 'yan bindiga suka fara ci gaba da barna a jihar Zamfara, inda hakan ya kai ga aka garkame kasuwannin shanu a wasu yankunan jihar ARewa.
Arewa
Samu kari