Yan ta'adda
Wasu miyagun yan bindiga sun kai mummunan farmaki har cikin gidan wani babban likita a jihar Kwara. Yan bindigan sun halaka likitan tare da sace diyarsa.
Manyan shugabannin yan ta'adda sun gamu da ajalinsu a shekarar 2023. Shugabannin yan ta'addan sun yi kaurin suna wajen aikata ayyukan ta'addanci.
A daren ranar Litinin ce wasu daga cikin mutane 11 da aka sace a kauyen Azzara da ke karamar hukumar Kachia suka tsere daga hannun 'yan bindiga a jihar Kaduna.
Majalisar dokokin jihar Sokoto ta amince da kudurin dokar kafa rundunar tsaro, domin magance matsalar rashin tsaro da ta dade tana addabar jihar.
Biyo bayan samun ingantaccen rahoto, rundunar 'yan sanda ta samu nasar gano wasu makamai da aka boye su a cikin wani buhu a jihar Delta, ana kan neman masu laifin.
Fursuna na karshe da hukumar kula da gidajen yarin jihar Katsina ta baza komar kama shi ya shiga hannu a Kaduna. A watan Oktoba ne fursunonin biyu suka tsere.
Mayakan Boko Haram sun kai sabon hari garin Chibok da ke a jihar Borno, inda suka kashe mutum biyu tare da jikkata wasu da dama. Sun kona gidaje masu yawa.
Rundunar yan sandan jihar Taraba sun samu nasarar sheke wasu yan bindiga mutum uku a wata fafatawa da suka yi. Yan sandan sun kuma ceto mutanen da suka sace.
Rundunar sojojin Najeriya ta daya ta sanar da cewa ta samu nasarar halaka wani dan bindiga guda daya da kwato makamai masu tarin yawa a wani samame a Kaduna.
Yan ta'adda
Samu kari