Yan ta'adda
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar fatattakar 'yan ta'adda a jihar Benue bayan sun yi musayar wuta. Jami'an tsaron sun kubutar da mutum biyu.
Rundunar 'yan sanda ta tabbatar da harin da 'yan bindiga suka kai a kauyen Ambe da ke karamar hukumar Sanga a jihar Kaduna. Rundunar ta ce an kama dan bindiga 1.
Sojojin Nijar sun cafke kasurgumin dan bindigar nan na Najeriya, Kachallah Mai Daji a Illela a lokacin da yake yunkurin satar dabbobi a kan iyakar Najeriya da Nijar.
Wasu bama-bamai da 'yan ta'adda suka dasa a kan hanya a jihar Borno sun yi sanadiyyar salwantar da rayukan mutum 11 tare da raunata wasu mutanen daban.
Gwamna Nasir Idris na jihar Kebbi ya sha alwashin sanya hannu a dokar kisan kai ga masu ba 'yan bindiga bayanan sirri wanda suke cutar da al'umma.
Rahotanni sun nuna cewa 'yan bindiga sun yi wa jami'an tsaron jihar Zamfara kwanton bauna a karamar hukumar Maradun. Sun hallaka jami'ai guda uku.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun kai harin ta'addanci a karamar hukumar Makarfi ta jihar Kaduna inda suka hallaka wani Dagaci tare da bankawa gidansa wuta.
Rahotanni sun nuna cewa wasu da ake kyautata zaton ‘yan ta’addan Boko Haram ne da suka tuba sun kona shingayen binciken kwakwaf na hukumar NDLEA da kwastam a Borno.
ACP Olumuyiwa Adejobi, a wata zantawa da manema labarai a jihar Kaduna, ya ce an kama Ibrahim Mandi, wanda ake zargin ya kitsa harin jirgin kasan Abuja-Kaduna.
Yan ta'adda
Samu kari