Muhimman Abubuwa 10 da Ya Kamata Ku Sani Game da Shugaba Tinubu Yayin da Ya Cika Shekara 72

Muhimman Abubuwa 10 da Ya Kamata Ku Sani Game da Shugaba Tinubu Yayin da Ya Cika Shekara 72

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, GCFR, shugaban Najeriya na yanzu, ya yi bikin cika shekaru 72 da haihuwa a ranar Jumu'a, 29 ga Maris, 2024.

Idan baku manta ba a kwanakin baya Shugaban Ƙasa Tinubu ya sanar da soke dukkan wani nau'i na biki ko taya murna a ranar da ya ƙara shekara, rahoton Tribune.

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu.
Bola Ahmed Tinubu ya cika shekara 72 a duniya Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
Asali: Facebook

A wannan lokaci na bikin cikarsa shekaru 72 a duniya, Legit Hausa ta tattaro muku abubuwa 10 da ya kamata ku sani game da Shugaba Tinubu, ga su kamar haka:

1. Mahaifarsa

An haifi Bola Ahmed Tinubu ne a jihar Osun, ɗaya daga cikin jihohin da ke shiyyar Kudu maso Yammacin Najeriya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

2. Karatunsa

Tinubu ya yi karatu a Ibadan, Legas, da jami’ar jihar Chicago, inda ya kammala digirinsa na farko a fannin Akanta a shekarar 1979.

Kara karanta wannan

Tinubu @ 72: Yadda aka taya Shugaban kasa murnar zagayowar ranar haihuwarsa

3. Tarihin ayyukan da ya yi

Shugaba Tinubu ya yi aiki a kamfanoni daban-daban na akantan kudi a Amurka kafin ya dawo kamfanin Mobil Oil Nigeria kuma daga karshe ya zama ɗan siyasa.

4. Yadda ya faro siyasa

Tinubu ya fara harkar siyasa ne tun a shekarun 1990, inda ya samu nasarar zama sanata karkashin inuwar Social Democratic Party (SDP), daga bisani ya zama jigo a siyasar Najeriya.

5. Sanatan Legas ta Yamma

Bola Tinubu ya riƙe kujerar Sanata mai wakiltar Legas ta Yamma daga ranar 5 ga Disamba, 1992, zuwa ranar 17 ga Nuwamba, 1993, karo na farko da ya fara siyasa a majalisa.

6. Gwamnan Legas

Ya yi gwamnan jihar Legas karo biyu a jere daga 1999 zuwa 2007 a karkashin inuwar jam’iyyar Alliance for Democracy (ADC).

7. Zama shugaban Najeriya

Ƙasa ɗa shekara ɗaya da ta wuce, Tinubu ya lashe zaben shugaban kasa a Najeriya bayan ƴa doke manyan abokan hamayya kamar Atiku Abubakar da Peter Obi.

Kara karanta wannan

Tinubu @72: Abin da Buhari ya fadawa Bola bayan ya kira shi musamman a waya

A ranar 29 ga watan Mayu, 2023 Tinubu ya karbi rantsuwar kama aiki a matsayin shugaban ƙasa na 16 a Najeriya.

8. Rayuwar iyalinsa

Duk da kasancewarsa mabiyin addidim Musulunci, Bola Ahmed Tinubu ya auri Remi Tinubu, wadda ta kai muƙami babba a addinin kirista. Oluremi da Bola Tinubu suna da yara hudu.

9. Kasuwanci

Tinubu babban ɗan kasuwa ne da ya shiga harkokin kasuwanci daban-daban, inda ya yi aiki a babban kamfani kuma yana da hannayen jari a kamfanoni da dama.

10. Jagoran yarbawa

A matsayin babban jigo a cikin kabilar Yarbawa, shugabancin Tinubu ya wuce siyasa kaɗai, yana da tasiri a fannin al’adu da zamantakewa.

FG ta bada tallafin aikin hajji

A wani rahoton kuma Gwamnatin tarayya ƙarƙashin Bola Tinubu ta tallafawa aikin hajjin bana da N90bn domin ragewa alhazai tsadar kuɗin kujera.

Wata majiya daga hukumar NAHCON ta bayyana cewa wannan tallafin ne ya sa aka nemi alhazai su cika N1.9m amma da sai ƙarin ya wuce haka.

Asali: Legit.ng

Online view pixel