NNPP Ta Yi Martani Ga Hukuncin Kotun Zaben Kano Da Ta Tsige Abba Gida Gida
- Shugabancin jam’iyyar New Nigeria Peoples Party bata ji dadin hukuncin kotun zaben jihar Kano ba
- Jam’iyyar NNPP a cikin wata sanarwa daga mukaddashin shugabanta na kasa, Abba Kawu Ali, ta ce hukuncin da kotun zaben ta yanke rashin adalci ne
- Jam’iyyar adawa a jihar Kano ta zargi kotun zaben da zalunci ta hanyar rage yawan kuri’u daga sakamakon NNPP domin ganin APC ta yi nasara a hukuncin da ta yanke
DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!
Jihar Kano - Jam'iyyar New Nigeria Peoples Party, (NNPP) ta bayyana hukuncin kotun zaben jihar Kano da ta tsige Gwamna Abba Kabir Yusuf, a matsayin "rashin adalci".
NTA News ta rahoto cewa mukaddashin shugaban jam'iyyar na kasa, Abba Kawu a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya yi zargin cewa saboda rashin adalci, kotun zaben ta cire kuri'u 165,663 daga sakamakon jam'iyyar don jam'iyyar APC mai mulki ta samu nasara.
![NNPP ta yi watsi da hukuncin kotun zabe NNPP ta yi watsi da hukuncin kotun zabe](https://cdn.legit.ng/images/1120/caa2958b95daed22.jpeg?v=1)
Asali: Twitter
Da yake rokon a kwantar da hankula a jihar Kano, mukaddashin shugaban ya kuma yi zargin cewa hukuncin cin zarafi ne ga kundin tsarin mulki, yana mai shan alwashin cewa za su daukaka kara a kan hukuncin.
Jaridar Punch ta rahoto cewa NNPP ta yi ikirarin cewa hukuncin kotun zaben ya maimaita abun da aka yi a zaben gwamnan na 2019, inda kotun zaben ta murde kuri'un mutane tare da bayar da shi ga wanda ya fadi zaben.
DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar
Bayan hukuncin kotu: An saka dokar kulle na awanni 24 a jihar Kano
A gefe guda, Legit Hausa ta rahoto a baya cewa an saka dokar kulle na awanni 24 a jihar Kano sakamakon hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben gwamna da ta tsige Gwamna Abba Kabir Yusuf. Hukuncin ya fara aiki daga karfe 6:00 na yammacin Laraba.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/72cc408013aa5569.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Manyan Dalilai 3 Da Suka Sa Kotun Zaben Kano Ta Tsige Abba Gida Gida Daga Kujerar Gwamna
Kwamishinan yan sandan jihar, Muhammad Usaini Gumel, a cikin wata sanarwa da ya sawa hannu, ya ce an baza tawagar jami'an tsaro na hadin gwiwa a fadin jihar don tabbatar da bin dokar kullen.
Gumel ya ce wannan matakin ya biyo bayan umurnin da suka samu ne daga gwamnatin jihar a kokarin da ake na tabbatar da zaman lafiya a gaba daya jihar.
Asali: Legit.ng