Tinubu Ya Lashe Zabe a Oyo, Ogun, Ondo, Ekiti, Kwara Yayin da Ake Ci Gaba Da Tattara Sakamako a Abuja

Tinubu Ya Lashe Zabe a Oyo, Ogun, Ondo, Ekiti, Kwara Yayin da Ake Ci Gaba Da Tattara Sakamako a Abuja

Jami'an hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) na ci gaba da tattara sakamakon zaben shugaban kasa na 2023 a matakan tarayya da na jiha.

Ana tattara sakamakon kasa a cibiyar taro ta kasa da ke Abuja karkashin jagorancin shugaban INEC, Mahmood Yakubu.

Kwamishinonin zabe na jiha ne ke tattara sakamakon jihohinsu mabanbanta.

Bola Tinubu, dan takarar shugaban kasa na APC a tsaye
Tinubu Ya Lashe Zabe a Oyo, Ogun, Ondo, Ekiti, Kwara Yayin da Ake Ci Gaba Da Tattara Sakamako a Abuja Hoto: @officialABAT
Asali: Twitter

Ana sa ran kwamishinonin zaben su dauki sakamakon kananan hukumomi a jiharsu zuwa cibiyar tattara sakamako na kasa a Abuja don yin lissafin karshe sannan shugaban INEC ya sanar da wanda ya yi nasara.

Zaben shugaban kasa na 2023: Tattara sakamakon kasa a Abuja

Zuwa yanzu, an tattara sakamakon jihohi 10 a matakin kasa a Abuja. Sune:

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: INEC Ta Bayyana Sakamakon Zaben Gwamna a Jihar Enugu Mai Cike da Ruɗani

  1. Jihar Ekiti
  2. Jihar Kwara
  3. Jihar Osun
  4. Jihar Ondo
  5. Jihar Ogun
  6. Jihar Oyo
  7. Jihar Yobe
  8. Jihar Enugu
  9. Jihar Lagos
  10. Jihar Gombe

Daga cikin jihohi 10 da aka lissafa a sama, dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar All Progressives Congress (APC), Bola Tinubu, ya lashe jihohi biyar da suka hada da Ekiti, Kwara, Ondo, Ogun da Oyo.

Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP) , Atiku Abubakar, ya lashe jihohi uku wato Osun, Gombe da Yobe.

Peter Obi, dan takarar shugaban kasa na Labour Party (LP) ya lashe jihohi biyu kacal wato Enugu da Lagos

Zuwa yanzu, Tinubu ya lashe jihohi kamar haka a zaben da aka tattara:

  1. Jihar Ekiti
  2. Jihar Ondo
  3. Jihar Kwara
  4. Jihar Ogun
  5. Jihar Oyo

Lura: Za mu ci gaba da tattaro jerin jihohin da Tinubu ya lashe yayin da ake ci gaba da tattara sakamakon zaben.

Asali: Legit.ng

Online view pixel