Dino Melaye Ya Kawo Wa Atiku Akwatinsa A Kogi, Duba Sakamakon

Dino Melaye Ya Kawo Wa Atiku Akwatinsa A Kogi, Duba Sakamakon

  • Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Peoples Democratic Party, PDP, ya kayar da Asiwaju Bola Ahmed Tinubu da Mr Peter Obi a jihar Kogi
  • Hakan na zuwa ne a yayin da Sanata Dino Melaye ya kawo wa Peoples Democratic Party, PDP akwatin zaben yankin sa a dukkan matakai a jihar
  • Dan majalisar na majalisa zubi ta 8 wanda ya kawo wa mai gidansa mazabarsa a jihar Kogi, ya yaba wa INEC kan amfani da na'urar BVAS

Jihar Kogi - Wani rahoto da jaridar Punch ta rahoto ya nuna cewa jigon jam'iyyar Peoples Democratic Party, PDP, daga jihar Kogi, Sanata Dino Melaye, ya kawo wa mai gidan sa, dan takarar shugaban kasa na PDP, Alhaji Atiku Abubakar.

Mai magana da yawun kwamitin yakin neman zabe na Atiku-Okowa ya lashe akwatin sa a Unit 004 Aiyetoro/IIuhagba mazaba ta 1.

Kara karanta wannan

Da Dumi-Dumi: Fafatawa Ta Yi Zafi, Atiku Abubakar Ya Samu Nasara a Jihar Taraba

Dino Melaye
Sanata Dino Melaye ya kawo wa Atiku akwatinsa: Hoto: @MobilePunch
Asali: Twitter

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Legit.ng ta tattaro cewa jam'iyyar ta PDP ta lashe mafi yawan kuri'u a zaben shugaban kasa, sanata da majalisar tarayya na wakilai.

Jam'iyyar ta PDP ta samu kuri'u 125 a zaben shugaban kasa, 116 a zaben kujerar sanata sai kuma kuri'u 103 a zaben yan majalisar wakilai na tarayya.

Ga cikakken sakamakon zaben a mazabar a kasa:

Mazabar Sanata Dino Melaye. UNIT 004 Aiyetoro/Iluhagba Ward 1

Shugaban kasa

PDP: 125

APC: 31

LP: 0

Sanata

PDP: 116

APC: 20

ADC: 34

LP: 0

Majalisar Wakilai na Tarayya

PDP: 103

APC: 17

ADC: 62

Peter Obi na LP ya kayar da Bola Tinubu a akwatin zaben shugaban kamfen dinsa

A wani rahoton kun ji cewa Gwamna Simon Lalong ya kasa kawo wa mai gidansa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu kuri'u mafi rinjaye a akwatinsa.

Kara karanta wannan

Zaben Shugaban Kasa: Peter Obi Ya Lallasa Atiku Da Tinubu a Jihar Cross River

Gwamnan Jihar Filato din shine shugaban kwamitin kamfen din shugaban kasa na jam'iyyar APC a zaben shekarar 2023.

Asali: Legit.ng

Online view pixel