Sauya Naira: Jerin Gwamnonin APC 14 Da Suka Daura Damarar Yakar Tsarin CBN

Sauya Naira: Jerin Gwamnonin APC 14 Da Suka Daura Damarar Yakar Tsarin CBN

  • Gwamnonin APC 14 ne suke takun saƙa da sabon tsarin CBN na sauya fasalin naira wanda ya jefa yan Najeriya cikin wahala.
  • Gwamna El-Rufai na Kaduna, Sanwo Olu na Legas, Yahaya Bello na Kogi da Matawalle na Zamfara na cikin gwamnonin
  • Bayan taron da suka gudanar jiya Lahadi, gwamnonin sun bayyana cewa bakin su ɗaya game da tsarin sauya kuɗin

Abuja - A bayyane take gwamnonin jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya suna adawa da sabon tsarin sauya naira kuma su ne a sahun gaba wajen yaƙar tsarin da CBN ya ɓullo da shi.

Gwamnonin da suka nuna adawarsu ga tsarin a fili na cikin waɗanda suka halarci taron gaggawa da shugaban APC na ƙasa, Abdullahi Adamu, ya kira ranar Lahadi, 19 ga watan Fabrairu, 2023.

Wasu bayanai da Legit.ng Hausa ta tattaro daga majiya mai ƙarfi sun haɗa jerin sunayen gwamnonin da suka halarci ganawar, waɗanda ke jan ragamar takun saƙa da CBN.

Kara karanta wannan

Karin Bayani: Tinubu Ya Kutsa Wurin Taron Shugaban APC da Gwamnoni Sama da 10, Bayanai Sun Fito

Gwamnonin APC.
Sauya Naira: Jerin Gwamnonin APC 14 Da Suka Daura Damarar Yakar Tsarin CBN Hoto: APCNigeria
Asali: Twitter

Gwamnonin sune kamar haka;

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

1. Gwamna Simon Bako Lalong na jihar Filato

2. Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa

3. Gwamna Abubakar Sani Bello na jihar Neja

4. Gwamna Malam Nasiru El-Rufai na jihar Kaduna

5. Gwamna Yahaya Bello na jihar Kogi

6. Gwamna Muhammad Inuwa Yahaya na jihar Gombe

7. Gwamna Mai Mala Buni na jihar Yobe

8. Gwamna Bello Matawalle na jihar Zamfara

9. Gwamna Biodun Oyebanji na jihar Ekiti.

10. Gwamna Babajide Sanwo-Olu na jihar Legas

11 Gwamna Atiku Bagudu na jihar Kebbi

12. Gwamna Muhammad Badaru na jihar Jigawa

13. Gwamna Aminu Bello Masari na jihar Katsina

14. Gwamna Hope Uzodinma na jihar Imo.

Wace matsaya gwamnonin APC suka cimma kan tsarin sauya naira?

Yayin ganawa da Abdullahi Adamu, gwamnonin karkashin inuwar kungiyar gwamnonin ci gaba na APC (PGF) sun bayyana a fili cewa duk bakinsu ɗaya kan batun karancin naira.

Kara karanta wannan

2023: Abinda Tinubu Ya Yiwa Borno Lokacin Boko Haram da Babu Wanda Ya Taɓa Mana, Gwamna Zulum

Da yake ƙarin haske kan haka, shugaban PGF, gwamna Atiku Bagudu ya ce baki ɗaya takwarorinsa sun amince da matsayar da taron ya cimmawa, kamar yadda Daily Trust ta rahoto.

A kalamansa, Bagudu ya ce:

"Duk bakin mu ɗaya, ƙungiyar gwamnonin ci gaba da kwamitin gudanarwa NWC duk jam'iyya ɗaya ce, dukkan mu abu ɗaya ne."

A wani labarin na daban kun ji cewa Bola Tinubu ya kutsa wurin taron shugaban APC da gwamnoni a Abuja

Sanata Abdullahi Adamu, ya gayyaci gwamnonin jam'iyyar APC zuwa zaman tattauna wa kan halin kuncin da sauya naira ya jefa 'yan Najeriya.

Taron wanda ya gudana jiya Lahadi, ya samu halartar gwamnoni sama da 10, ba zato sai ga Bola Tinubu ya shiga cikin ganawar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262