Kujerar Sanatan Kebbi: Aliero Zai Gwabza da Bagudu Yayin da Kotun Koli Ta Tabbatar da Shi Dan Takarar PDP

Kujerar Sanatan Kebbi: Aliero Zai Gwabza da Bagudu Yayin da Kotun Koli Ta Tabbatar da Shi Dan Takarar PDP

  • Kotu ta tabbatar da Adamu Aliero a matsayin sahihin dan takarar sanatan Kebbi ta tsakiya karkashin inuwar jam'iyyar PDP
  • Kotun koli ta zartar da hukunci inda ta soke hukuncin kotun daukaka kara na ayyana Saidu Haruna a matsayin dan takarar PDP
  • Za a fafata tsakanin Aliero da gwamnan jihar Kebbi mai ci, Atiku Bagudu wanda ke takarar kujerar a APC

Kotun koli ta tabbatar da Sanata Muhammad Adamu Aliero a matsayin dan takarar jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP) na sanaa mai wakiltan yankin Kebbi ta tsakiya, jaridar Daily Trust ta rahoto.

A ranar Litinin ne kwamitin mutum biyar karkashin jagorancin Justis China Centus Nweze ya jingine hukuncin kotun daukaka kara, wacce ta fara jingine karar da Aliero ya daukaka inda yake kalubalantar hukuncin babbar kotun tarayya kan zaben fidda gwanin jam'iyyar.

Kara karanta wannan

'Barin Zance: Gwamnonin APC 3 Sun Jagoranci Tinubu Domin Kai Wa Buhari Ziyarar Dannar Ƙirji

Atiku Bagudu da Adamu Aliero
Kujerar Sanatan Kebbi: Aliero Zai Gwabza da Bagudu Yayin da Kotun Koli Ta Tabbatar da Shi Dan Takarar PDP Hoto: Daily Trust
Asali: UGC

Da suke yanke hukunci, Kwamitin alkalan karkashin jagorancin Justis Amina Augue, sun ce karar da Aliero ya daukaka yana mai kalubalantar ayyana Saidu Haruna a matsayin dan takarar PDP na kujerar sanata na bisa daidai.

Hakazalika, babban kotun ta tabbatar da zaben Dr Abubakar Yahaya Abdullahi a matsayin dan takarar PDP na sanata mai wakiltan Kebbi ta arewa a zaben ranar 25 ga watan Fabrairu.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Za a fafata tsakanin Sanata Aliero na PDP da Gwamna Bagudu na APC

Aliero zai gwabza da Gwamna Atiku Bagudu, wanda ke takarar kujerar sanata mai wakiltan Kebbi ta tsakiya a karkashin inuwar jam'iyyar All Progressives Congress (APC), rahoton Aminiya.

Akwai yiwuwar Kwankwaso ya koma bayan Atiku a zabe mai zuwa, Jigon arewa

A wani bari na daban, hasashe sun nuna cewa dattawa, sarakuna na manyan masu ruwa da tsaki a yankin arewacin kasar sun fara tattaunawa da Sanata Rabiu Kwankwaso game da yadda zaben shugaban kasa na 2023 za ta kasance.

Kara karanta wannan

Sabon Matsala Ga Atiku Yayin Da Kotu Ta Amince A Dauki Muhimmin Mataki Kan Dan Takarar Na PDP

Wani jigon arewa da aka sakaya sunansa ya ce wannan tattaunawar yunkuri ne na lallashin Kwankwaso tare da shawo kansa kan ya janye sannan ya yi hadaka da dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar.

An yanke wannan shawara ce duba ga yadda tsagin gwamnonin G-5 karkashin jagorancin Gwamna Nyesom Wike suka taso Atiku a gaba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng

Tags: