Ministan Buhari Ya Yi Wa Dino Melaye Alkawarin Wata Babban Alfarma Idan Ya Kammala Wa'adinsa A 2023

Ministan Buhari Ya Yi Wa Dino Melaye Alkawarin Wata Babban Alfarma Idan Ya Kammala Wa'adinsa A 2023

  • Ministan Buhari Ya Yi Wa Dino Melaye Alkawarin Wata Alfarma Da Zarar Ya Sauka Daga Mukaminsa A 2023
  • Festus Keyamo, karamin ministan kwadago da ayyukan yi, ya yi wa Dino Melaye alkawarin da zai cika a shekarar 2023
  • Ministan ya ce zai yi wa tsohon dan majalisar rajista a makarantar koyon waka don ya goge kamar sauran mawakan kasar

Keyamo da Melaye sun fara musayar maganganu tun bayan nada su a matsayin kakakin yakin neman zaben Bola Tinubu da Atiku Abubakar

Ba a fara kamfen din zaben shugaban kasa na shekarar 2023 ba a hukumance amma ana ta musayar maganganu tsakanin Sanata Dino Melaye da Minista Festus Keyamo.

Keyamo Da Melaye
2023: Abin Da Zan Yi Wa Dino Melaye Bayan Na Sauka Daga Mukamin Minista, Keyamo Ya Yi Zafafan Maganganu. Hoto: (Photo: Festus Keyamo Esq, Dino Melaye).
Asali: Facebook

A wani hira da aka yi da shi a Arise TV a ranar Litinin 8 ga watan Agusta, Keyamo ya yi ikirarin cewa yana kewan kotu kuma zai koma can da zarar wa'adinsa a matsayin karamin ministan kwadago da samar da ayyuka ya kare a 2023.

Kara karanta wannan

2023: Ku kwantar da hankali, za a yi zaben 2023 ba tare da wata matsala ba, hafsan tsaro

Ministan ya yi ikirarin cewa idan hakan ta faru, zai tabbatar ya yi wa Melaye rajista a makarantar waka, ya kara da cewa kakakin kamfen din na Atiku Abubakar yana bukatar malami sosai.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Keyamo ya cigaba da cewa da tunda farko Melaye ya taho wurinsa, da yanzu ya yi nasara sosai a wakokinsa da barkwanci.

Ya yi alkawarin zai raini tsohon dan majalisar kamar yadda ya raini wasu mawaka da a yanzu suna moriyar sana'ar.

Kalamansa:

"Zan koma aikin lauya na bayan wa'adi na ta minista ta kare kuma zan tabbatar na yi wa Dino Melaye rajista a makarantar waka, yana bukatar hakan sosai."

A Aljanna Ne Kawai Ba Za A Samu Matsalar Tsaro Ba, Yanzu Kuma Duniya Muke, Ministan Buhari, Keyamo

A wani rahoton, Festus Keyamo, karamin ministan kwadago da samar da ayyuka, ya ce ba za a iya amfani da 'hare-haren' da aka kaiwa wasu sassan kasar ba a matsayin 'mizani' na cewa gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta gaza.

Kara karanta wannan

Rikicin Atiku da Wike: Jam'iyyar PDP ta dage zaman NEC saboda ta'azzarar rikicin gida

Keyamo ya yi wannan jawabin ne a hirar da aka yi da shi a Channels Television a ranar Juma'a, The Cable ta rahoto.

A cikin yan makonnin baya-bayan nan, munanan hare-hare sun karu a sassan kasar har da babban birnin tarayya, Abuja.

Asali: Legit.ng

Online view pixel