Sanatan Kebbi ta tsakiya: Alaka ta yi tsami tsakanin Aliero da Gwamna Bagudu kan wanda zai mallaki tikitin APC

Sanatan Kebbi ta tsakiya: Alaka ta yi tsami tsakanin Aliero da Gwamna Bagudu kan wanda zai mallaki tikitin APC

  • Siyasar APC a Kebbi na kara zafi kan wanda zai mallaki tikitin jam’iyyar na sanata mai wakiltan jihar ta tsakiya
  • Ana fafutukar tikitin ne tsakanin Sanata Adamu Aliero wanda shine a kan kujerar a yanzu da Gwamna Atiku Bagudu wanda zai kammala wa’adin mulkinsa na biyu
  • Rikicinsu ya samo asali ne tun bayan da aka sauke mambobin jam’iyyar masu biyayya ga Aliero daga shugabancin jam’iyyar a jihar

Kebbi - Sabon rikici ya kunno kai a jam’iyyar All Progressives Congress (APC) reshen jihar Kebbi kan kudirin Gwamna Abubakar Bagudu na son zama sanata.

Gwamnan wanda zai kammala wa’adin mulkinsa na biyu a watan Mayun 2023, yana neman tikitin jam’iyyar na sanata mai wakiltan yankin Kebbi ta tsakiya, Daily Trust ta rahoto.

Sanata Adamu Aliero ne a kan kujerar a yanzu haka kuma yana neman zarcewa a karkashin inuwar jam’iyyar ta APC.

Kara karanta wannan

Wani dan takarar shugaban kasa ya karaya ya kai karar PDP kan kudin fom N40m

Sanatan Kebbi ta tsakiya: Alaka ta yi tsami tsakanin Aliero da Gwamna Bagudu kan wanda zai mallaki tikitin APC
Sanatan Kebbi ta tsakiya: Alaka ta yi tsami tsakanin Aliero da Gwamna Bagudu kan wanda zai mallaki tikitin APC Hoto: Daily Trust
Asali: UGC

Alaka ta yi tsami a tsakanin Aleiro da Bagudu tun bayan tarukan jam’iyyar mai mulki a jihar. Shugabannin biyu na fafatawa kan wanda zai ja ragamar tsarin jam’iyyar.

Dan majalisar ya koka kan tursasa yan takara a yayin taronsu da tsige mambobin jam’iyyar da ake ganin suna biyayya gare shi a tsarin shugabannin jam’iyyar.

Da yake magana a yayin gangamin siyasa a watan Janairu, Aliero ya ce rikicin siyasa na jiran APC a jihar idan jam’iyyar ta ki yin adalci a tsakanin mambobinta.

Ya ce:

“Za a samu mummunan sakamako idan APC a jihar Kebbi ta kasa yin adalci ga kowa. A yayin babban taron jam’iyyar da ya gabata an cire wasu ‘ya’yan jam’iyyar a matsayin shugabanni saboda son rai yayin da aka daura wasu a kan mukamansu. Ba za mu bari hakan ya kasance ba kuma ba za mu lamunci hakan ba.”

Kara karanta wannan

2023: Ganduje ya bayyana ainahin dalilin da yasa ya tsayar da Nasiru Gawuna don ya gaje sa

Masu sa ido kan harkokin siyasa a jihar sun ce gwamnan jihar yana da damar lashe tikitin takarar Sanata na jam'iyyar.

APC ta sake kara wa'adin sayar da foma-foman takara

A wani labarin, mun ji cewa jam'iyyar APC ta sake tsawaita wa'adin sayar da fom din takara da sauran shagulgulan da ta sa a gaba gabanin babban zaben 2023.

Wannan sauyi na zuwa ne daidai lokacin da wasu jiga-jigan jam'iyyar suka fara mayar da cikakkun foma-foman takara ga jam'iyyar a makon nan.

APC ta kara wa'adin sayar da fom din daga ranar 10 ga watan Mayu zuwa Alhamis, 12 ga watan Mayu, yayin da ta dage mayar da foma-fomai zuwa gobe Juma'a, 13 ga watan Mayu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng