Jagororin APC 20 da suka sa baki aka yi wa ‘Yan kasa da shekara 40 rangwamen fam

Jagororin APC 20 da suka sa baki aka yi wa ‘Yan kasa da shekara 40 rangwamen fam

  • Shugaban matasan APC na kasa ya bada sanarwar cewa za ayi wa duk wani matashi rangwamen sayen fam din shiga takara a jam’iyyar mai mulki
  • Dayo Israel ya bayyana wannan nasara da aka samu a shafinsa na Twitter a ranar Laraba. Hakan na zuwa ne bayan taron NEC da aka gudanar a Abuja
  • Kamar yadda Dayo Israel ya fada, duk wanda bai kai shekara 40 ba, zai saye fam din ne a rabin farashin da za a saidawa sauran masu neman shiga takara

The Cable ta ce sabon shugaban matasan na jam’iyyar APC mai mulki ya yi kira ga mutane cewa su yi amfani da wannan dama da ba a taba samun irin ta ba.

Kara karanta wannan

An samu ‘Yan siyasa 2 da suka saye fam a PDP, za su jarraba sa’a kan Zulum a 2023

Hakan na nufin matasan da ke neman takarar gwamna za su biya N25m a maimakon N50m. Masu harin kujerar majalisar wakilan tarayya za su kashe N5m.

Sannan kuma ‘yan kasa da shekara 40 za su saye fam din takarar majalisar dokoki a kan N1m. Mai neman zama Sanata a zaben 2023 zai saye fam a kan N10m.

Legit.ng Hausa ta fahimci Israel da mataimakinsa kadai ne masu kananan shekaru da suka halarci taron majalisar kolin na jam’iyyar APC mai mulki a Abuja.

Wadanda suka yi kokari

Israel ya ambaci duk wadanda suka taimaka wajen ganin an yi wa matasa wannan rangwame a taron da aka gudanar. Ga su nan kamar yadda ya jero su a Twitter:

1. Shugaban majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila

2. Shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan

Kara karanta wannan

Kofar rashawa: 'Yan Najeriya sun kadu da jin farashin fom din takarar shugaban kasa N100m a APC

3. Gwamnan jihar Legas, Jide Sanwo-Olu

4. Gwamna jihar Kogi, Yahaya Bello

5. Gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma

Jagororin APC
Taron majalisar NEC APC Hoto: @OfficialAPCNig
Asali: Facebook

Sauran wadanda suka taka rawar gani sun hada da

6. Shugaban jam’iyya, Abdullahi Adamu

7. Sakataren jam’iyya, Iyiola Omisore

8. Gwamna Simon Lalong

9. Gwamna Rotimi Akeredolu

10. Gwamna Badaru Abubakar

11. Gwamna Gboyega Oyetola

12. Gwamna Aminu Masari

13. Gwamna Bello Matawalle

14. Gwamna Kayode Fayemi

15. Mataimakin Gwamnan jihar Enugu

16. Mataimakin Gwamnan jihar Kano

Sai kuma

17. Mataimakin shugaban majalisar wakilai, Ahmed Wase

18. Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Ovie Omo Agege

19. Mataimakin shugaban kasa da

20. Mai girma shugaban kasa

Matasa za su amfana

Da farko, Muttaqa Abdul Hadi Dabo wanda yake da niyyar fitowa takarar gwamnan Kaduna ya yi mamakin jin yadda jam’iyyar APC ta lafta kudin fam a N50m.

Sardaunan a bari ya huce ya ce zai bunkasa ilmi, samar da aikin yi, yaki talauci, inganta harkar noma da samar da ruwan sha idan ya zama Gwamnan Kaduna.

Shi kuma hadimin shugaban kasa, Bashir Ahmaad mai neman yin takarar kujerar ‘dan majalisar tarayya a APC ya bada shela a Facebook cewa zai je sayen fam.

Kara karanta wannan

Yanzu-yanzu: N100m zamu sayar da Fom din takarar kujerar shugaban kasa, Jam'iyyar APC

Ahmaad mai shekara 31 yana cikin wadanda za su ci moriyar wannan sauki da aka yi wa matasa. Zai nemi kujerar Gaya/Albasu/Ajingi a majalisar wakilai a APC.

Asali: Legit.ng

Online view pixel