Da Dumi-Dumi: Sanata Mai Wakiltar Mazabar Shugaba Buhari ya fice daga APC, ya koma PDP

Da Dumi-Dumi: Sanata Mai Wakiltar Mazabar Shugaba Buhari ya fice daga APC, ya koma PDP

  • Sanata Ahmad Babba Kaita mai wakiltar Katsina ta arewa a Majalisar dattawa ta kasa ya fice daga APC ya koma PDP
  • Rahoto ya nuna cewa Kaita ya miƙa takardar murabus daga APC a gundumarsa dake yankin karamar hukumar Kankiya ranar Talata
  • Wannan dai na zuwa ne bayan alaka ta yi tsami tsakanin sanatan da gwamnan Katsina, Aminu Bello Masari

Katsina - Ɗan majalisa mai wakiltar mazaɓar Katsina ta arewa a majalisar dattawan Najeriya, Sanata Ahmad Babba Kaita ya sauya sheƙa daga APC zuwa PDP.

Katsina ta arewa wacce ta kunshi yankin Daura da kewayenta, nan ne yankin mazaɓar shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, kamar yadda Aminiya ta rahoto.

Sanata Ahmad Babba Kaita.
Da Dumi-Dumi: Sanata Mai Wakiltar Mazabar Shugaba Buhari ya fice daga APC, ya koma PDP Hoto: Sulaiman Aminu Sasma/facebook
Asali: Facebook

Bayanai sun nuna cewa Sanata Babba Kaita ya miƙa takardar murabus daga APC a gundumarsa dake ƙaramar hukumar Kankiya ta jihar Katsina ranar Talata, 19 ga watan Afrilu, 2022.

Kara karanta wannan

Da Dumi-Dumi: Tsohon na kusa da Buhari ya fice daga jam'iyyar APC, ya jero dalilai

Meyasa Sanatan ya ɗauki matakin barin APC?

Mutane na gani matakin ficewa daga APC da Sanata Babba Kaita ya ɗauka ba zai rasa alaƙa da rashin jituwar dake tsakaninsa da gwamnan Katsina, Aminu Bello Masari ba.

Babba Kaita ya jima yana sukar lamirin gwamnatin Katsina, musamman kan ƙin gudanar da zaɓen kananan hukumomi tun bayan kafa gwamnatin a 2015.

Sai dai a yan kwanakin nan a cikin wannan watan na Afrilu, aka gudanar da zaɓen kannan hukumomi a faɗin jihar Katsina, wanda hukumar zaɓe ta ce APC ta lashe dukkan kujeru.

A wani labarin kuma Daga Karshe, Minista Ngige ya ayyana shiga takarar shugaban kasa, ya faɗi wasu kalmomi

Bayan dogon lokaci ana yaɗa jita-jita, Ministan Kwadugo da samar da aikin yi, Chris Ngige, ya ayyana shiga tseren gaje Buhari.

Kara karanta wannan

Kannywood 2023: Jarumi Lukman na Shirin 'Labarina' ya fito takarar siyasa a Kano

Dakta Ngige, wanda ya yaba wa gwamnatin APC, ya ce shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari bai ba mutane kunya ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262